• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunwa Ta Kazanta A Sansanonin ‘Yan Gudun Hijira Tun Bayan Da Majalisar Dinkin Duniya Ta Dakatar Da Ayyukanta

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
3 months ago
in Labarai
0
Yunwa Ta Kazanta A Sansanonin ‘Yan Gudun Hijira Tun Bayan Da Majalisar Dinkin Duniya Ta Dakatar Da Ayyukanta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan gudun hijira a jihohin Borno da Binuwai na fama da matsanancin yunwa sakamakon alamun da ke nuna cewa manyan hukumomin Majalisar Dinkin Duniya na janye ayyukansu a Nijeriya saboda raguwar kudaden gudanar, kamar yadda bincike ya nuna.

 

Hukumomin dai su ne ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai kula da ayyukan jin kai (UNOCHA) da kuma hukumar samar da abinci ta duniya (WFP).

  • Seyi Tinubu Ya Musunta Zargin Kamawa Da Bayar Da Cin Hanci Ga Shugaban NANS
  • An Cafke Saurayi Bisa Zargin Yi Wa ‘Yar Budurwarsa Fyade A Bauchi

‘Yan gudun hijira a wasu sansanonin da ‘yan jarida suka ziyarta a jihohin Borno da Benuwai, sun bayyana fargabar cewa matakin da hukumomin samar da agajin gaggawa da kula bala’o’i biyu suka dauka na iya kara janyo kalubalen harkokin jin kai da ke fuskantarsu.

A sansanonin ‘yan gudun hijiran da ke Borno wadanda suka bar gidajensu sakamakon ta’addancin ‘yan kungiyar Boko Haram da kuma wadanda suke Benuwai da ya faru sakamakon hare-haren ‘yan bindiga a kauyuka daban-daban.

Labarai Masu Nasaba

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Ministan harkokin jin kai da rage radadin talauci na UNOCHA, Farfesa Nentawe Goshwe, ya sanar da yunkurin hukumar na ficewa daga Nijeriya. Ya shaida hakan ne a yayin taron kara wa juna sani kan tsarin da za a dauka a Nijeriya, wanda aka gudanar a cibiyar yaki da ta’addanci ta kasa, ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro a Abuja.

A cikin wata wasika da aka yada a shafin intanet na hukumar a ranar 11 ga Afrilu, shugaban hukumar ta UNOCHA, Tom Fletcher ya ba da sanarwar yanke ayyuka sakamakon karancin kudade na kusan dala miliyan 60 a shekarar 2025.

Hukumar ta ce za ta rage ayyukanta a Nijeriya, Kamaru, Kolombiya, Eritriya, Iraki, Libya, Pakistan, Turkiyya da Zimbabwe, da nufin ba da fifikon da maida cikakken karfi a sauran wuraren da take gudanar da ayyukanta.

Kazalika, ita ma hukumar samar da abinci ta duniya (WFP) a ranar 28 ga watan Maris ta yi gargadin cewa mutane miliyan 58 na cikin hadarin rasa taimakon ceton rai a cikin ayyukan 28 na ceto da hukumar take yi sakamakon raguwar kudade a cikin manyan masu ba da agaji.

Mataimakiyar Babban Darakta na WFP, Rania Dagash-Kamara kan hadin gwiwa da kirkire-kirkire, ta ce hukumar na fuskantar raguwar kudaden tallafin da kashi 40 cikin 100 a shekarar 2025, idan aka kwatanta da na bara.

Sai dai abu mafi muni, ‘yan gudun hijira sun nuna gayar damuwa bisa halin da suke ciki. Wasu ‘yan gudun hijira a Muna, Maiduguri, da ke Jihar Borno, sun shaida cewar tsawon watanni suna fuskantar matsalolin yunwa sakamakon janye ayyukan tallafi na abinci a sansanonin ‘yan gudun hijira da ke jihar.

Shugaban sansanin Muna, Malam Abatcha Mustapha, ya ce ‘yan gudun hijira na cikin matsanancin rayuwa na yunwa kuma ba za su iya ci gaba da kasancewa ba tare da tallafin abinci ba.

“Mun samu kanmu a cikin tsaka mai wuya lokacin da suka daina kawo mana abinci, sai a ranar Sallah ne hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA) ta kawo mana abinci. Mutanenmu suna cikin matsanancin yanayi. Muna zaman jiran umarni daga wajen gwamna domin komawa asalin gidajenmu a kananan hukumomi Dikwa da Mafa.”

Ya ce akwai ‘yan gudun hijira sama da mutane 44,000 a wannan sansanin kuma a shirye suke su koma gidajensu na asali domin ba karamar wahala suke sha a inda suke a halin yanzu ba.

Shugaban nakasassu a sansanin Abiso Kadi ya ce, “Tun daga lokacin da hukumar NEMA da sauran masu sa baki suka janye tallafin abinci na wucin gadi a wannan sansanin, rayuwa ta yi mana wuya, ba ni da aikin da zan yi a nan a matsayina na makaho, abin da na dogara da shi shi ne tallafin da hukumar NEMA ta bayar.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Seyi Tinubu Ya Musunta Zargin Kamawa Da Bayar Da Cin Hanci Ga Shugaban NANS

Next Post

Layukan Dogo Na Kasar Sin Sun Gudanar Da Sufurin Miliyoyin Fasinjoji A Ranar Farko Ta Hutun ‘Yan Kwadago

Related

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

1 hour ago
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
Labarai

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

2 hours ago
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule
Labarai

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

3 hours ago
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC
Labarai

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

4 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

5 hours ago
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi
Labarai

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

7 hours ago
Next Post
Layukan Dogo Na Kasar Sin Sun Gudanar Da Sufurin Miliyoyin Fasinjoji A Ranar Farko Ta Hutun ‘Yan Kwadago

Layukan Dogo Na Kasar Sin Sun Gudanar Da Sufurin Miliyoyin Fasinjoji A Ranar Farko Ta Hutun ‘Yan Kwadago

LABARAI MASU NASABA

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.