A baya-bayan nan aka kammala tattaunawar Shangri-La ta bana. Kuma idan aka kwatanta da na shekarun baya, dabarar yaudara kan tekun kudancin kasar Sin da kasar Philippines ta nuna yayin taron, na bukatar kasa da kasa su sa mata ido sosai.
Dabarar ba wani abu ba ne, face neman kasa da kasa su tausaya mata ta hanyar karairayi domin dakile halastattun hakkokin Sin a tekun. Amma akwai adalci a zukatan jama’a, kuma ba za a taba jirkita karya da gaskiya ba. Rikici kan teku tsakanin Sin da Philippines, ba batu ne na wanda ya fi girma ko kankanta ba, batu ne na daidai da akasinsa.
Hakika yayin tattaunawar ta Shangri-La, ministan tsaron Philippines ya yi kokarin fakewa da cewa a shirye kasarsa take ta zama abun da Amurka za ta yi amfani da shi wajen dakile kasar Sin, yana mai kokarin kare hakikanin gaskiyar cewa tuni Philippines din ta rasa ’yancinta. Sai dai sanarwar hadin gwiwa ta taron ministocin tsaron Amurka da Japan da Australia da Philippines ta nuna cewa, Amurka da kasashen yamma sun amince tare da goyon baya da shirya yaudarar ta gwamnatin Philippines kan batun tekun kudancin Sin, domin goyon bayan manufar da Amurka ke ikirari kan yankin tekun Indiya da Pasifik. Philippines na kai kanta ga hadari, kuma wannan dabarar yaudara ba za ta taba yin nasara ba. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp