Tare da kwararru a fannin makamashi, rukunin Dangote na da muhimmiyar rawar da zai taka wajen ba da gudummawa ta fuskar bunkasa wuraren da aka gano mai kwanan nan a yankin Bida na Jihar Neja.
Da yake jawabi ga shugabannin masana’antu a taron bikin baje kolin kasuwancin kasa ta Jihar Neja da aka yi a Minna, Gwamna Bago ya sanya Jihar Neja a matsayin wata cibiya ta kasuwanci” dangane da bunkasar mai na a tafkin ‘Bida Basin’, musamman ya yi kira ga kamfanoni masu zaman kansu da su zuba jari da kwarewa a aikin hako mai da iskar gas a jihar.
- Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
- Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Gwamna Umaru Muhammed Bago wanda ya samu wakilcin Hamza Bello Sarki babban sakataren ma’aikatar kasuwanci da masana’antu da saka hannun jari, ya amince da kwazon da kamfanin DDangote ke da shi wajen gudanar da manyan ayyukan masana’antu, inda ya ba da misali da nasarar isar da matatar mai a kasar nan daya tilo da aka yi a Nijeriya a matsayin shaida ta kwarewar fasaha da kuma kyakkyawan aiki.
Rukunin Dangote shi ne kan gaba wajen daukar nauyin bikin baje kolin kasuwanci na Nijar na 2025.
Gwamnan ya bayyana gano mai yankin na Bida Basin a matsayin tikitin Jihar Neja na bunkasar tattalin arziki, da cin nasara ga abokan hulda.
Wani rahoto na binciken yanayin kasa na shekarar 2023 ya gano bututun mai guda 17 da za aiya cin kasuwa da shi a Jihar Neja, tare da kiyasin da aka yi na zai hako iskar gas har ta tsawon shekara 70.
Basin na Bida, wanda ya ratsa sassan jihohin Neja da Kwara, an gano shi a matsayin yankin da ke kwararo albarkatun mai mai cike da fa’ida.
Wakilin rukunin Dangote, Mista Hashem Ahmed, ya ce kamfanin yana zuba jari sosai a Jihar Neja, ya kara da cewa a shirye yake ya hada gwiwa da jihar domin ba ta damar bunkasa abubuwan da ta ke da su.
“Kamfanin Shinkafa na Dangote da ke Wushishi idan an kammala shi zai inganta noman shinkafar cikin gida da kuma rage asarar da ake samu bayan girbi, muna kuma aiki kafada da kafada da ofishin gwamna kan shirin samar da abinci na Neja, shirin noma da ke taka muhimmiyar rawa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp