• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
in Kasashen Ketare
0
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafofin yada labarai na Syria da ma wasu na yankin Gabas ta Tsakiya sun koka kan yadda sabuwar gwamnatin Syria ta yi gum da bakinta tun bayan barkewar yaki tsakanin Isra’ila da Iran.

Haka nan wasu na mamakin yadda jiragen saman Isra’ila ke ratsawa ta sararin samaniyar Syriya domin kai hare-hare a cikin Iran.

  • Wang Yi: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Rika Tuntubar Juna Domin Kaucewa Rashin Fahimta
  • Za A Kara Amfani Da Rokar Long March-2F Wajen Harba ‘Yan Sama Jannati Zuwa Tashar Sararin Samaniyar Sin

Amfani da sararin samaniyar Syria da jiragen Isra’ila ke yi da kuma amfani da sararin na Syria da Iran ke yi tana harba makamai zuwa Isra’ila ya haifar da asarar rayuka daga dukkanin bangarorin biyu, kuma duk da haka gwamnatin ta Syria ba ta ce uffan ba.

Jaridu da dama a yankin sun yi sharhi kan lamarin, yayin da wasu masana ke cewa rashin tsoma bakin Syriya na nufin mataki ne na tsayawa a tsakiya, wasu kuma na ganin kasar na kallon dukkanin kasashen biyu ne a matsayin makiyanta.

Wani babban jami’in gwamnatin Syriya ya yi watsi da zargin cewa Syriyar na barin Isra’ila na amfani da sararin samaniyarta wajen samun bayani kan makaman da Iran ke harbawa.

Labarai Masu Nasaba

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Har yanzu dai gwamnatin Syriya ba ta komai ba game da barna da hasarar rayuka da makamai da kuma jiragen da ake amfani da su da ta sararin samaniyarta ke haifarwa ba.

Shafin Intanet na kafar Enab na kasar Syria ya wallafa wani labari a ranar 15 ga watan Yuni game da shirun da gwamnatin Syriya ta yi kan karakainar da jiragen yaki da makamai masu linzami ke yi a sararin samaniyar kasar.

Wani mai sharhi ya fada wa Enab cewa gwamnatin Syriya ta yanke shawarar tsayawa tsakiya kan lamarin ne kasancewar tana daukar Isra’ila da Iran a matsayin abokan gabarta.

Ya ce: “Babu daya daga cikinsu da za ka bayyana shi a matsayin abokin al’ummar Syriya, kuma dukkaninsu sun taka rawa wajen lalata kasar Syriya.”

Iran na daga cikin manyan kasashen da suka taimaka wa tsohon shugaban Syriya Bashar al-Assad, ita kuma Isra’ila ta kaddamar da daruruwan hare-hare ta sama kan Syriya, kuma ta jibge sojojinta a yankunan tudun mun tsira tun cikin watan Disamba bayan tuntsurar da gwamnatin Assad.

Ya ce gwamnatin Syria a yanzu ta shagalta ne da kokarin daidaita lamurra a cikin gida da kuma karfafa dakon dangantakarta da Turkiyya da kuma kasashen yankin Gulf.

Jaridar da ke kare muradun yankin Larabawa ta ‘Middle East Eye’ ta ruwaito cewa shugaban Turkiyya Receb Tayyib Erdogan ne ya shawarci sabon shugaban Syria Ahmed al-Sharaa cewa kada ya tsoma kansa cikin rikicin.

Saba ka’idar sararin samaniya

Kafar yada labarai ta Syria ta buga rahotanni da dama tana cewa Isra’ila da Iran na karya ka’idojin amfani da sararin samaniyarta, inda ta ce jirage marasa matuka da kuma makamai masu linzami da dama sun fada cikin kasar.

Kafar yada labarai ta Syria – SANA – ta ruwaito cewa wani jirgi mara matuki ya fada kan wani gida a birnin Tartus, kuma daga baya an tabbatar da cewa matar ta rasu sanadiyyar raunukan da ta samu.

Haka nan kafar yada labaran ta SANA ta ruwaito cewa wasu jirage marasa matuka sun fada kan gidajen al’umma a birnin Daraa kuma wani makamai mai linzami ya fada gefen Damascus, babban birnin kasar, inda makamin ya bar wani katon rami.

Sai dai shirun da gwamnatin Syria ta yi kan wannan lamari ya ja hankalin kafafen yada labarai a cikin kasar da kuma kasashen Larabawa.

Yawancin jaridun sun ja hankalin al’ummar kasar cewa kada su kusanci wauraren da makaman ke fadawa.

Sai dai wata majiya ta gwamnati ta karyata ikirarin jaridar Al-Watan, wadda ta ce Ahmed al-Sharaa ya amince wa Isra’ila ta yi amfani da sararin samaniyar Syria wajen samun bayanai kan tafiyar makaman da Iran ke harbawa.

Gidan talabijin na Syria TD da ke da mazauni a Turkiyya ya tattauna da wani mai sharhi, wanda ya ce ya kamata Syria ta kai korafin wajen Majalisar Dinkin Duniya, sannan kuma ta yi amfani da kasashe kawayenta wajen hana karya ka’idojin amfani da sararin samaniyarta.

 

Gidan talabijin dain ya ce yakin na Iran da Isra’ila ya yi cikas ga zirga-zirgar jirage zuwa kasar da kuma datse kai tallafi ga al’ummar kasar masu bukata.

 

Wata jarida ta yankin Larabawa, Al-Kuds Al-Arabi ta ce akwia damuwa kan cewa yakin zai kara raunana tattalin arzikin Syria wanda ba ya da karfi, inda ta ce darajar kudin kasar ta Syria ya fadi da kashi 10 cikin dari tun bayan fara yakin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IranIsraelSyria
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Next Post

Za a Binne ÆŠantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Related

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka
Kasashen Ketare

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

4 days ago
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?
Kasashen Ketare

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

1 week ago
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa
Kasashen Ketare

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

1 week ago
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
Kasashen Ketare

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

2 weeks ago
Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

3 weeks ago
Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu
Kasashen Ketare

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

3 weeks ago
Next Post
Za a Binne ÆŠantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne ÆŠantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga'ibi A Kano

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.