• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

by Sulaiman
4 months ago
Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, yana da cikakken ƙudiri na tabbatar da ’yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi domin zurfafa dimokiraɗiyya da kuma hanzarta cigaba a matakin ƙasa.

 

Ministan ya bayyana haka ne a Abuja a ranar Juma’a, lokacin da ya karɓi tawagar Ƙungiyar Tsofaffin Kansiloli ta Ƙasa wadda ta kai masa ziyarar ban-girma a ofishin sa.

  • Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

Ya ce: “Ƙananan hukumomi su ne mataki na uku na gwamnati kuma su ne suka fi kusa da jama’a. Shi ya sa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu cikin hikimar sa ya sake duba batun ’yancin cin gashin kai ga ƙananan hukumomi.”

 

LABARAI MASU NASABA

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

Ya tunatar da cewa a bara, Antoni-Janar na Ƙasa kuma Ministan Shari’a ya nemi fassarar doka daga Kotun Ƙoli, inda kotun ta tabbatar da cewa kundin tsarin mulki ya tanadi ’yancin cin gashin kai ga ƙananan hukumomi.

 

“An samu hukunci daga babbar kotun ƙasa da ke nuna cewa kundin tsarin mulkin mu ya tanadi buƙatar ƙananan hukumomi su samu ’yancin kai – su kasance masu cikakken iko da damar aiki a fannoni daban-daban, ko siyasa ko kuma kuɗi,” inji shi.

 

A cewar sa, bai wa ƙananan hukumomi dama za ta ƙarfafa dimokiraɗiyya a matakin ƙasa da kuma samar da cigaba a cikin al’umma.

 

Idris ya nuna damuwa kan yadda tsarin ƙananan hukumomi ya raunana a tsawon lokaci, yana nuni da cewa tsarin ya sha bamban da yadda aka tsara shi tun farko.

 

“Tsawon shekaru, mun shaida yadda ƙarfin ikon ƙananan hukumomi yake ci gaba da raguwa fiye da yadda kundin tsarin mulki ya tanada,” inji shi.

 

Ya ƙara da cewa Shugaban Ƙasa Tinubu, wanda gwani ne wajen kare dimokiraɗiyya, yana da tabbacin cewa ƙarfafa wannan mataki na gwamnati yana da matuƙar muhimmanci domin cigaban dimokiraɗiyya a ƙasar nan.

 

“Shugaban Ƙasa ɗan dimokiraɗiyya ne na gaske, kuma yana ganin cewa domin dimokiraɗiyyar mu ta kai inda muke fata, dole ne a ƙarfafa wannan mataki na gwamnati,” inji shi.

 

Ya buƙaci gwamnoni da su mara wa ƙoƙarin Shugaban Ƙasa baya wajen dawo wa da ƙananan hukumomi ƙarfin su yadda masu tsara kundin tsarin mulki suka nufa tun farko.

 

Ministan ya kuma gode wa tsofaffin kansilolin bisa jajircewar su wajen kare dimokiraɗiyya, tare da roƙon su da su isar da saƙon gwamnatin Tinubu ga jama’ar ƙasa.

 

“Ina roƙon ku da ku tallafa wa sauye-sauyen Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu. Ba a tsara su domin wahalar da ‘yan Nijeriya ba. E, da farko za su iya kasancewa masu tsauri amma kamar yadda Shugaban Ƙasa ya faɗa, tattalin arzikin mu yana samun daidaito,” inji shi.

 

Ministan ya bayyana cewa cire tallafin fetur da daidaita farashin musayar kuɗaɗe da aka yi sun haifar da gagarumar riba, wanda hakan ya haifar da ninka kuɗaɗen da ake raba wa jihohi da ƙananan hukumomi domin aiwatar da ayyukan cigaba.

 

Ya ƙara da cewa kafa kwamitocin cigaba a kowane yanki na ƙasa wani mataki ne na ganin cigaba ya isa kowane lungu da saƙo na Nijeriya.

 

Tawagar tsofaffin kansilolin ta karrama ministan da Lambar Yabo ta Maida Hankali Kan Jama’a, inda shi kuma ya nuna godiya tare da cewa hakan zai ƙara masa ƙwazo wajen yi wa al’umma hidima.

 

A nasa jawabin, Sakatare na biyu na ƙungiyar, Mista Cole Michaels, ya yaba da irin yadda ministan yake farfaɗo da hukumomin da ke ƙarƙashin sa domin wayar da kan jama’a kan manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Tinubu.

 

Ya ce an bada lambar yabon ne saboda gudunmawar sa wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya a ƙasar.

 

Tawagar ta ƙunshi wakilai daga jihohi daban-daban a ƙasar nan, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙungiyar, Mista Auwal Kassim Hassan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata
Labarai

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Next Post
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

LABARAI MASU NASABA

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.