• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kawo Dauki Don Magance Tsadar Kudin Zuwa Aikin Hajjin Bana

by Abubakar Ibrahim
1 year ago
in Labarai
0
hajjin 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kowace shekara, al’ummar Musulmi suna gudanar da aikin Hajji domin cika daya daga cikin shikashikan addininsu guda biyar. Abu ne wanda kowane Musulmi ke son cimmawa, akalla sau daya a rayuwarsa, yayin da kuma wani mai kumbar susa yake da burin ya sake komawa ya kara yi. Duk da haka, wanda ke da hali ne kadai aka wajabta wa yin wannan tafiya zuwa kasa mai tsarki don sauke farali.

A Nijeriya, tuni shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2024 suka kankama. Sai dai kuma ana ta samun wani babban kalubale, musamman na kudin tafiya aikin na maniyyata. Duk da kokarin da Hukumar Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) take yi na ganin an shawo kan tsadar kudin tafiya Hajjin bana, farashin ya yi tashin gwauron zabi wanda ba a taba ganin irinsa a baya ba. Lamarin ya jefa maniyyata cikin halin kaka-ni-ka-yi da tsananin rudani.

  • IFAD Da Gwamnatin Tarayya Sun Yi Hadaka Don Bunkasa Aikin Noma A Arewa
  • Sin Da EU Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Domin Inganta Musaya Tsakanin Jama’arsu

Duk da ce-ce-ku-cen da ake yi game da karin kudin, matsalar ta samo asali ne daga wasu manyan abubuwa guda biyu — su ne hauhawar farashin Dalar Amurka da kuma jinkiri ko kin biyan kudin aikin Hajji kan lokaci daga maniyyata.

Idan an tuna, tun da farko sai da hukumar NAHCON ta kayyade mafi karancin kudin ajiya na aikin Hajjin bana a kan naira miliyan hudu da rabi (N4.5m), aka ce za a fadi farashi na karshe bisa la’akari da farashin Dala a lokacin da za a kammala lissafa kudin. Saboda sauyin farashin Dala, ya zama tilas hukumar ta yi kari kan farashin ta na farko.
Karin da aka yi dai sakamakon faduwar darajar Naira ne. Duk da kokarin da Shugaban NAHCON, Malam Jalal Ahmad Arabi ya yi na ganin farashin zuwa aikin Hajjin bana bai canza ba, an bukaci maniyyata da su biya naira 4,899,000 ga wadanda suka fito daga Kudu, wadanda suka fito daga Arewa kuma naira 4,699,000, sannan naira 4,679,000 ga wadanda suka fito daga yankin Yola da Maiduguri.

Matsalar da Nijeriya ta kwashe watanni tana fama da ita na canjin kudaden waje ya sa tilas hukumar ta nemi wadanda suka biya kudin ajiya na kimanin naira miliyan 4.9 da su cika naira 1,918,032.91, daidai da farashin kudaden waje na yanzu. Hakan ya sa adadin kudin da masu niyyar zuwa aikin Hajjin za su biya ya zama naira miliyan 6.8 ga ‘yan ajiya. Su kuwa sababbin masu son biyan kudin za su biya naira 8,225,464.74 daga maniyyata daga Arewa, yayin da maniyyatan Kudu za su biya naira 8,454,464.73. Kuma hukumar ta ce ana bukatar a kammala biyan wadannan kudaden kafin karfe 11:59 na dare a ranar 28 ga Maris, 2024.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hukumar NAHCON ta yi kokari da dama wajen ganin maniyyata sun samu saukin farashi a bana. Misali, a farkon wannan shekarar shugaban hukumar ya jagoranci tawagar jami’ansa zuwa kasar Saudiyya inda suka tattauna da masu gidajen haya da otal-otal da motocin haya a garuruwan Makka da Madina da Masha’ir don su rage kudi ga maniyyatan Nijeriya, kuma sun samu matukar nasarar hakan. Tattaunawar ta haifar da raguwar farashin jirgi da masauki da sauran su. In da ba domin zuwan da suka yi ba, to da kudin zuwa Hajji da ake magana yanzu ya zarta haka.

Duk da matakan ragin kudaden da NAHCON ta dauka da suka hada da neman tallafin gwamnatocin jihohi da masu hannu da shuni ga alhazan su, da kuma shiga tsakani da Gwamnatin Tarayya ta yi, gazawar maniyyatan wajen cika wa’adin da aka bayar na biyan kudin aikin Hajjin da aka kara shi ma ya haifar da karin kudin zuwa aikin Hajjin bana. Rashin biyan cikakken kudi a kan lokacin da aka tsara ya haifar da tsawaita wa’adin, kuma yayin da aka tsawaita wa’adin, farashin kudaden waje na hauhawa. Hakan ne ya sa kudin aikin Hajjin ya karu.

Ba shakka, karin kudin aikin Hajji ya zama babban kalubale ga maniyyatan Nijeriya a bana. A halin da ake ciki, akwai alamun da yawa daga cikin maniyyatan da suka biya kudin ajiya ba za su iya biyan cikon naira miliyan 1.9 da ake bukata ba, yayin da su kuma sababbin biya da yawansu sai dai ido, musamman a cikin takaitaccen wa’adin da NAHCON ta bayar. Hakan zai sa maniyyata su rasa damar zuwa Saudiyya gaba daya.

Don haka, ya zama wajibi ga Gwamnatin Tarayya da gwamnatocin jihohi da masu hannu da shuni da su shigo cikin al’amarin, su ba da tallafi don sassauta nauyin da ke kan maniyyatan, tare da daukar matakan da za su sa maniyyata na nan gaba su samu saukin yin wannan tafiya mai alfarma. Kada a nade hannu a zuwa wa matsalar ido, musamman a cikin wannan takaitaccen lokaci.

* Abubakar Ibrahim dalibin digiri na biyu ne a Sashen Koyon Aikin Jarida a Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bassirou Diomaye Faye: Daga Kurkuku Ya Zama Shugaba Mafi Karancin Shekaru A Afirka

Next Post

Abin Da Masu Hannu Da Shuni Ya Kamata Su Rika Yi A Kan Rabon Zakkah

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

3 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

4 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

5 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
Aikin hajji
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

10 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

11 hours ago
Next Post

Abin Da Masu Hannu Da Shuni Ya Kamata Su Rika Yi A Kan Rabon Zakkah

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.