• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Wannan Karo, Sun Karkata Hankali Ga Barkonon Jihar Xinjiang

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Ra'ayi Riga
0
A Wannan Karo, Sun Karkata Hankali Ga Barkonon Jihar Xinjiang
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jihar Xinjiang na daga cikin sassan kasar Sin da kafafen yada labarai na kasashen yamma suke son baza karairayi a kai. Idan ba a manta ba, a kimanin wata guda da ya wuce, sun ba da rahotanni game da wai “ana bautar da laburori” a gonakin noman auduga da tumatir na jihar Xinjiang, ga shi a kwanakin nan, sun karkata hankali ga barkonon jihar, inda wasu kafafen yada labarai na kasashen yamma suka ce, wai kayayyakin barkonon da ake sayarwa a cikin kantunan Amurka da Burtaniya na kunshe da barkonon da ake nomawa a jihar Xinjiang, wadanda ya yiwu ake samarwa bisa aikin tilas, don haka sun yi kira ga kamfanonin kasashen yamma da su daina yin amfani da barkonon jihar Xinjiang. 

Amma da gaske ne ana bautar da leburori a jihar Xinjiang? 

A hakika, aiki ne ya kai ni jihar Xinjiang sau da dama. Birnin Wusu da ke arewacin jihar na daga cikin muhimman sassan da ke samar da tumatir a jihar, kuma na je birnin a watan Agustan bara, inda na gane ma idona yadda na’urorin tsinkar tumatir ke shan aiki a cikin gonakin tumatir. Mai gonar malam Zhang Tongquan ya ce min, fadin gonakinsa ya kai kimanin eka 133, kuma mutane hudu ne kawai ke kula da su, sabo da kusan na’urori ke dukkan ayyukan da ke shafar shuka tsiron tumatir da ma tsinkarsu. Ya ce, na’urar guda daya na iya tsinkar tumatir daga gonakin da fadinsu ya kai kimanin eka 6.7 cikin yini guda, wato aikin da kimanin leburori 150 suke yi ke nan, kuma hakan na iya rage kudin da yake biya wajen ayyukan tsinkar tumatir da kimanin kudin Sin Yuan miliyan daya.

Duk wanda ya taba shiga gonakin jihar Xinjiang ya san cewa, ko aikin noman auduga ko tumatir ko kuma barkono, kusan ana amfani da na’urori wajen gudanar da dukkan ayyukan. Alkaluman da aka samar sun shaida cewa, kimanin kaso 85% na ayyukan diban auduga a jihar Xinjiang, na’urori ne ke yi su, adadin da har ya kai 100% a akasarin sassan noman tumatir da kuma barkono. Gaskiya ita ce tushen ayyukan samar da rahotanni, ai su kafafen yada labarai da suka yada karairayi game da “aikin tilas a jihar Xinjiang” abin da su ke yi ba aikin jarida ba ne, a maimakon haka, tamkar suna tsara wasannin kwaikwayo ne, amma ko wannan aikin ma ba su cancanta ba, sabo da a jihar Xinjiang da ake yawan amfani da na’urori, ta yaya za a samu “aikin tilas”, ko suna nufin tilasta wa na’urori aiki ake yi?

To, amma me ya sa kafafen yada labarai na kasashen yamma ba su gaji da shafa wa jihar Xinjiang kashin kaza ba? 

Labarai Masu Nasaba

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Bari mu dauki misali da auduga. Amurka na daga cikin muhimman sassan duniya da ke samar da auduga, wadda a baya ta kasance kasar da ta fi samar da auduga a duniya, sai dai kasar Sin ta maye gurbinta daga baya sakamakon yawan auduga masu inganci da ta samar, lamarin da ya zamanto barazana ga ayyukan samar da auduga a kasar da ma kasuwarta. Don haka, Amurka ta yi iyakacin kokarin dakile ayyukan samar da auduga a jihar Xinjiang, kasancewarta jihar da ta fi samar da auduga a kasar Sin. Hasali ma dai, ita Amurka ta saba da irin aiki, kasancewar ta taba sanya wa kasar Uzbekistan takunkumi ta fannin aikin samar da auduga bisa sunan wai “ana bautar da leburori yara a kasar”, kuma sanin kowa ne Uzbekistan kasa ce da ta shahara da noman auduga a tsakiyar Asiya.

Baya ga tattalin arziki, akwai kuma dalili na siyasa. Saurin bunkasuwar kasar Sin cikin ‘yan shekarun baya ta sa Amurka da wasu kasashen yamma matukar damuwa, don haka suke iyakacin kokarin neman dakile ci gabanta, kuma yadda suke sanya takunkumi a kan kayayyakin da ake samarwa a jihar Xinjiang na daga cikin matakan da suka dauka, a yunkurin lalata bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma a jihar, ta yadda za su cimma burinsu na yi wa kasar Sin tarnaki. Wani jami’in karamin ofishin jakadancin kasar Amurka da ke birnin Guangzhou na kudancin kasar Sin ya taba bayyana a fili cewa, “Dukkanmu na sane da cewa, Xinjiang ba ta da matsala, amma baza jita-jita game da matsalolin hakkin dan Adam a jihar Xinjiang mataki ne mai amfani, ta hakan za mu iya tsunduma kasar Sin cikin mawuyacin hali, kuma hakan zai amfanawa kasar Amurka.”

Auduga da tumatir da barkono da aka samar a jihar Xinjiang, kayayyaki masu inganci ne da suka yi suna har a fadin duniya, haka kuma ginshiki ne ga al’ummar jihar wajen samun kudin shiga. Amma yadda Amurka da kasashen yamma suke fakewa da sunan “kare hakkin dan Adam” wajen shafawa jihar Xinjiang kashin kaza, ya sa su rasa ayyukan yi, matakin da a hakika ya keta hakkin dan Adam na al’ummar jihar. Alkaluman da aka samar sun shaida cewa, ya zuwa karshen bara, sama da kamfanoni 100 a jihar sun daina ayyukansu sakamakon takunkumin da kasashen yamma suka sanya musu, kuma yawan mutanen da suke ayyukan da suka shafi sassaka da tufafi da abubuwan ado ya ragu da kimanin 28.6%.

Karya fure take ba ta ‘ya‘ya, in ji Bahaushe. Karairayin da ake kokarin yadawa game da Xinjiang ba za su kai ga canza gaskiyar yanayin da ake ciki na samun bunkasuwar tattalin arziki da walwalar rayuwar al’umma a jihar ba, haka kuma ba za su iya hana al’ummar jihar da ta kasar Sin baki daya ‘yancinsu na samun ci gaba da rayuwa mai walwala ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Zan Yi Ƙasa A Gwiwa Ba Wajen Ceto Manchester City Ba – Guardiola

Next Post

Sin Ta Gabatar Da Sabon Samfurin Jirgin Kasa Mai Matukar Sauri

Related

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

4 days ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

6 days ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

2 weeks ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

2 weeks ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

2 weeks ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Next Post
Sin Ta Gabatar Da Sabon Samfurin Jirgin Kasa Mai Matukar Sauri

Sin Ta Gabatar Da Sabon Samfurin Jirgin Kasa Mai Matukar Sauri

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.