• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnoni 13 Na Fuskantar Rashin Tabbas A Kotun Ƙoli

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Gwamnoni 13 Na Fuskantar Rashin Tabbas A Kotun Ƙoli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla gwamnonin Nijeriya 13 ne ke jiran sauraron sakamakon karshe game da shari’o’in da suka biyo bayan zabukan da aka gudanar a jihohin kasar saboda makomar gwamnonin 13 ya ta’allaka ne kan sakamakon karar da suka shigar ko ake kalubalantar nasararsu a kotun koli.

Jihohin da abin ya shafa da kotun daukaka kara ke kalubalantar hukuncin da ‘yan takarar jam’iyyun adawa a zaben gwamna da aka yi ranar 18 ga watan Maris sun hada da Jihar Kano da Plateau da Abia da Delta da Cross River da Rivers da Lagos da Sokoto da Nasarawa da Benue da Akwa Ibom da Taraba da kuma Jihar Bauchi.

  • Kotu Ta Kori Karar Abba K. Yusuf Ta Tabbatar Da Hukuncin Kotun Zabe Da Ya Tabbatar Da Gawuna
  • DA DUMI-DUMI: Kotu Ta Kori Gwamna Abba Gida-Gida Ta Tabbatar Da Nasarar Gawuna

Tawagar lauyoyin da ke kare wasu daga cikin bangarorin da abin ya shafa a jihohin sun shigar da kara gaban kotu a hukumance kamar yadda a ranar Juma’ar da ta gabata, yayin da wasu suka sha alwashin garzayawa kotun koli da ake sa ran za su gabatar a cikin makon nan don shigar da kara kotun.

Ana kuma sa ran babban Alkalin Alkalan Nijeriya, Mai Shari’a Olukayode Ariwoola, zai ja kunnen alkalai don su fara sauraron kararrakin nan ba da dadewa ba.

Wannan shi ne mataki na karshe na kararrakin kujerun gwamnoni a jihohin da aka gudanar da zabe ranar 18 ga watan Maris.

Labarai Masu Nasaba

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ma’ana, duk gwamnan da ya rasa shari’ar a kotun koli, ya bar ofishinsa kenan.

Wannan ya sha bamban da sakamakon da aka samu kan takaddamar zabe a kananan kotuna na kotun sauraren kararrakin zabe da kuma kotun daukaka kara da ta bai wa gwamnoni damar ci gaba da rike mukamansu ba tare da la’akari da ko sun ci ko sun fadi ba.

Matakin da kotun koli ta yanke kan kararrakin da suka taso daga hukuncin da kananan kotuna suka yanke kan zaben gwamnoni a kasar shi ne zai zama na karshe.

A tsakanin shekarar 1999 zuwa 2019, gwamnonin da ba su gaza takwas ba ne, wadanda aka kalubalanci zabensu a kotun koli, aka kuma tsige su daga mukamansu na gwamnoni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ElectionGwamnoniKotun KoliNigeriaNijeriyaShari'aSupreme Court
ShareTweetSendShare
Previous Post

Adadin Masu Kamuwa Da Cutar Numfashi Ya Ragu A Sin

Next Post

Sin Ta Zartas Da Dokar Sanya Ido Da Jagorancin Cibiyoyin Hada-hadar Biyan Kudade Da Ba Na Banki Ba

Related

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

6 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

7 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

19 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

21 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

1 day ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

1 day ago
Next Post
Sin Ta Zartas Da Dokar Sanya Ido Da Jagorancin Cibiyoyin Hada-hadar Biyan Kudade Da Ba Na Banki Ba

Sin Ta Zartas Da Dokar Sanya Ido Da Jagorancin Cibiyoyin Hada-hadar Biyan Kudade Da Ba Na Banki Ba

LABARAI MASU NASABA

Gwamnoni

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Gwamnoni

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.