• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

by Abba Ibrahim Wada
3 weeks ago
in Wasanni
0
Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Peter Rufa’i, daya daga cikin fitattun masu tsaron raga na tawagar Super Eagles ta Nijeriya, kuma fitaccen dan wasan kwallon kafa na Afirka, ya rasu a ranar Alhamis, 3 ga watan Yuli, 2025, ya bar tarihi da ke ci gaba da zaburar da ‘yan wasan kwallon kafa da masoya.

Jajircewa da jagoranci, na daga cikin halayen da Rufai ya bari a cikin zukatan wadanda suka yi rayuwar kwallo tare da shi, da kuma dubban ‘yan Nijeriya masu sha’awar kwallon kafa da suka samu damar kallon wasanninsa a lokacin da yake sanye da riga mai tambarin shaho kuma yake tsaye a bakin ragar Nijeriya domin tare duk wani hari irin na wannan wasa ta kwallo mai miliyoyin masoya a fadin duniya, “Dodo Mayana”, kamar yadda ake kiran sa ya kasance babban jigo a fagen kwallon kafa a Nijeriya.

  • Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC
  • NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Bayan gudummawar da ya bayar a filin wasa, rayuwar Rufa’i ta kasance wani nau’i na musamman na da ke dauke da juriya, sadaukarwa, da sha’awar wasan.

A yayin da ‘yan Nijeriya da ma duniyar kwallon kafa ke juyayin rashin sa, ga abubuwa 10 da ya kamata ku sani game da marigayi golan Super Eagles.

1. Peter Rufa’i Ya Fito Daga Gidan Sarauta

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

An haifi Peter Rufa’i a ranar 24 ga watan Agusta, 1963, a Oshodi, Legas, a wani gidan sarautar gargajiya, Mahaifinsa shi ne sarkin kabilar Idimu a Jihar Legas, duk da hasashen da ake yi na cewa zai yi gadon sarautar gidansu, Rufa’i ya yi watsi da sarautar don ci gaba da fuskantar abin da yake sha’awa wato kwallon kafa.

2. Ya yi Wasa A Manyan Kungiyoyin Kwallon Kafa A Kasashen Turai

Rufa’i ya fara sana’ar kwallon kafa a kungiyoyin gida Nijeriya kamar Storeery Stores da Femo Scorpions kafin ya tsallaka zuwa kasar waje, ya taka leda a kungiyoyi a kasar Benin (Dragons de l’Ouémé), Belgium (Lokeren, Beberen), Netherlands (Go Ahead Eagles), Portugal (Farense, Gil Bicente), da Spain (Hércules, Deportibo La Coruña), inda ya samu gogewa a bangaren da yake na mai tsaron raga.

3. Ya Taimakawa SC Farense Wajen Samun Damar Buga Kofin Turai (UEFA)

A lokacin kakar shekarar 1994–95, Rufa’i ya taka rawar gani wajen taimaka wa kulob din SC Farense na Portugal samun nasarar shiga gasar cin kofin UEFA na farko, ya ci gaba da zama a kungiyar inda aka zura masa kwallaye 38 kacal a wasanni 34 da ya buga a wannan kakar wasan.

4. Shine Mai tsaron Ragar Nijeriya Na Farko A Gasar Kofin Duniya

Rufa’i ya buga wa Nijeriya wasanni 65 na kasa da kasa, kuma shi ne mai tsaron raga na farko da Nijeriya ta zaba a gasar cin kofin duniya na FIFA a shekarun 1994 da 1998, ya kuma taka muhimmiyar rawa a gasar cin kofin nahiyar Afirka da Nijeriya ta yi a kasar Tunisia a shekarar 1994.

5. Ya Taba Ci Wa Nijeriya Kwallo

Yayin da ba kasafai ake samun mai tsaron raga ya ci kwallo a wasan kwallon kafa ba, Rufa’i ya zura wa Nijeriya kwallo a bugun fenareti a wasan da suka doke Habasha (Ethiopia) da ci 6-0 a wasannin neman gurbin shiga gasar AFCON a shekarar 1993, ita ce kadai kwallon da ya taba ci wa Nijeriya, kuma ta kasance daya daga cikin lokutan da ba zai taba mantawa da shi ba a rayuwarsa.

6. Ana Yi Masa Lakabi Da “Dodo Mayana”

Masoya nayi wa Rufa’i lakabi da “Dodo Mayana” saboda zafin nama da yadda yake tare kwallaye cikin kwarewa, lakabin ya zama tamkar wani kamanceceniya da yake yi da Dodo na asali duba da yadda yake yin abin da ba ayi tsammanin cewa zai iya yi ba.

7. Ya Yi Makarantar Aikin Horarwa Domin Samun Lasisin Horarwa

Bayan ya yi ritaya daga buga kwallon kafa, Rufa’i ya dawo aji a shekarar 2023, inda ya shiga Cibiyar kula da wasanni ta kasa da ke Legas don samun takardar cancantar zama koci, yana daga cikin babban kokarin da ya yi wajen ganin ya ci gaba da taimaka wa matasa masu tasowa wajen kwarewa da jagoranci a harkar kwallon kafa.

8. Ya Kafa Makarantar Kwallon Kafa ta Staruf

Mai himma wajen bunkasa matasa, Rufa’i ya kafa makarantar horar da kwallon kafa ta Staruf a Legas, har ila yau, ya kasance mai bayar da shawara akan a saka wasanni cikin jadawalin koyarwa a Nijeriya, ya kuma bukaci iyaye a Nijeriya da su yi kokarin cikar burin ‘ya’yansu na zama cikakkun yan kwallo tare da karatun Boko a lokaci guda.

9. Yana Da Matukar Jajircewa Akan Abin Da Ya Saka A Gaba

Rufa’i ya bayyana cewar tsawon shekaru 20 fa ya shafe a matsayin dan kwallon kafa bai rasa nasaba da yadda yake da jajircewa a duk abin da ya saka a gaba, inda yake cewa ina bayar da himma fiye da kashi 100 a koda yaushe, wadannan dabi’un, in ji shi, sun taimaka masa ya yi nasara a kasashe da dama da kuma fuskantar matsin lamba.

10. Yaba Karbar Laifinsa Idan Akayi Rashin Nasara

Duk da rawar da ya taka a fagen kwallon kafa a tsawon lokaci, rashin nasarar da Nijeriya tayi a hannun Denmark da ci 4-1 a gasar cin kofin duniya na shekarar 1998 a zagaye na 16 na daya daga cikin mafi munin wasannin da Rufa’i ya buga, ya bayyana shi a matsayin wasan da ya fi zafi a


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GolaNijeriyaPeter Rufai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Next Post

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Related

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace
Wasanni

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

8 hours ago
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?
Wasanni

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

2 days ago
Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray
Wasanni

Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

4 days ago
Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
Wasanni

Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta

5 days ago
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
Wasanni

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

5 days ago
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON
Wasanni

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

6 days ago
Next Post
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.