• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

byAbba Ibrahim Wada
3 months ago
Peter

Peter Rufa’i, daya daga cikin fitattun masu tsaron raga na tawagar Super Eagles ta Nijeriya, kuma fitaccen dan wasan kwallon kafa na Afirka, ya rasu a ranar Alhamis, 3 ga watan Yuli, 2025, ya bar tarihi da ke ci gaba da zaburar da ‘yan wasan kwallon kafa da masoya.

Jajircewa da jagoranci, na daga cikin halayen da Rufai ya bari a cikin zukatan wadanda suka yi rayuwar kwallo tare da shi, da kuma dubban ‘yan Nijeriya masu sha’awar kwallon kafa da suka samu damar kallon wasanninsa a lokacin da yake sanye da riga mai tambarin shaho kuma yake tsaye a bakin ragar Nijeriya domin tare duk wani hari irin na wannan wasa ta kwallo mai miliyoyin masoya a fadin duniya, “Dodo Mayana”, kamar yadda ake kiran sa ya kasance babban jigo a fagen kwallon kafa a Nijeriya.

  • Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC
  • NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Bayan gudummawar da ya bayar a filin wasa, rayuwar Rufa’i ta kasance wani nau’i na musamman na da ke dauke da juriya, sadaukarwa, da sha’awar wasan.

A yayin da ‘yan Nijeriya da ma duniyar kwallon kafa ke juyayin rashin sa, ga abubuwa 10 da ya kamata ku sani game da marigayi golan Super Eagles.

1. Peter Rufa’i Ya Fito Daga Gidan Sarauta

LABARAI MASU NASABA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

An haifi Peter Rufa’i a ranar 24 ga watan Agusta, 1963, a Oshodi, Legas, a wani gidan sarautar gargajiya, Mahaifinsa shi ne sarkin kabilar Idimu a Jihar Legas, duk da hasashen da ake yi na cewa zai yi gadon sarautar gidansu, Rufa’i ya yi watsi da sarautar don ci gaba da fuskantar abin da yake sha’awa wato kwallon kafa.

2. Ya yi Wasa A Manyan Kungiyoyin Kwallon Kafa A Kasashen Turai

Rufa’i ya fara sana’ar kwallon kafa a kungiyoyin gida Nijeriya kamar Storeery Stores da Femo Scorpions kafin ya tsallaka zuwa kasar waje, ya taka leda a kungiyoyi a kasar Benin (Dragons de l’Ouémé), Belgium (Lokeren, Beberen), Netherlands (Go Ahead Eagles), Portugal (Farense, Gil Bicente), da Spain (Hércules, Deportibo La Coruña), inda ya samu gogewa a bangaren da yake na mai tsaron raga.

3. Ya Taimakawa SC Farense Wajen Samun Damar Buga Kofin Turai (UEFA)

A lokacin kakar shekarar 1994–95, Rufa’i ya taka rawar gani wajen taimaka wa kulob din SC Farense na Portugal samun nasarar shiga gasar cin kofin UEFA na farko, ya ci gaba da zama a kungiyar inda aka zura masa kwallaye 38 kacal a wasanni 34 da ya buga a wannan kakar wasan.

4. Shine Mai tsaron Ragar Nijeriya Na Farko A Gasar Kofin Duniya

Rufa’i ya buga wa Nijeriya wasanni 65 na kasa da kasa, kuma shi ne mai tsaron raga na farko da Nijeriya ta zaba a gasar cin kofin duniya na FIFA a shekarun 1994 da 1998, ya kuma taka muhimmiyar rawa a gasar cin kofin nahiyar Afirka da Nijeriya ta yi a kasar Tunisia a shekarar 1994.

5. Ya Taba Ci Wa Nijeriya Kwallo

Yayin da ba kasafai ake samun mai tsaron raga ya ci kwallo a wasan kwallon kafa ba, Rufa’i ya zura wa Nijeriya kwallo a bugun fenareti a wasan da suka doke Habasha (Ethiopia) da ci 6-0 a wasannin neman gurbin shiga gasar AFCON a shekarar 1993, ita ce kadai kwallon da ya taba ci wa Nijeriya, kuma ta kasance daya daga cikin lokutan da ba zai taba mantawa da shi ba a rayuwarsa.

6. Ana Yi Masa Lakabi Da “Dodo Mayana”

Masoya nayi wa Rufa’i lakabi da “Dodo Mayana” saboda zafin nama da yadda yake tare kwallaye cikin kwarewa, lakabin ya zama tamkar wani kamanceceniya da yake yi da Dodo na asali duba da yadda yake yin abin da ba ayi tsammanin cewa zai iya yi ba.

7. Ya Yi Makarantar Aikin Horarwa Domin Samun Lasisin Horarwa

Bayan ya yi ritaya daga buga kwallon kafa, Rufa’i ya dawo aji a shekarar 2023, inda ya shiga Cibiyar kula da wasanni ta kasa da ke Legas don samun takardar cancantar zama koci, yana daga cikin babban kokarin da ya yi wajen ganin ya ci gaba da taimaka wa matasa masu tasowa wajen kwarewa da jagoranci a harkar kwallon kafa.

8. Ya Kafa Makarantar Kwallon Kafa ta Staruf

Mai himma wajen bunkasa matasa, Rufa’i ya kafa makarantar horar da kwallon kafa ta Staruf a Legas, har ila yau, ya kasance mai bayar da shawara akan a saka wasanni cikin jadawalin koyarwa a Nijeriya, ya kuma bukaci iyaye a Nijeriya da su yi kokarin cikar burin ‘ya’yansu na zama cikakkun yan kwallo tare da karatun Boko a lokaci guda.

9. Yana Da Matukar Jajircewa Akan Abin Da Ya Saka A Gaba

Rufa’i ya bayyana cewar tsawon shekaru 20 fa ya shafe a matsayin dan kwallon kafa bai rasa nasaba da yadda yake da jajircewa a duk abin da ya saka a gaba, inda yake cewa ina bayar da himma fiye da kashi 100 a koda yaushe, wadannan dabi’un, in ji shi, sun taimaka masa ya yi nasara a kasashe da dama da kuma fuskantar matsin lamba.

10. Yaba Karbar Laifinsa Idan Akayi Rashin Nasara

Duk da rawar da ya taka a fagen kwallon kafa a tsawon lokaci, rashin nasarar da Nijeriya tayi a hannun Denmark da ci 4-1 a gasar cin kofin duniya na shekarar 1998 a zagaye na 16 na daya daga cikin mafi munin wasannin da Rufa’i ya buga, ya bayyana shi a matsayin wasan da ya fi zafi a

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar
Wasanni

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Next Post
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version