• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 10 Game Da Karin Tsintsiyar Hannu

by Sani Anwar
8 months ago
in Labarai
0
Abubuwa 10 Game Da Karin Tsintsiyar Hannu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

1- Kari wani dunkulallen bulli ne mai dan taushi ko tauri da kan fito a sassan jiki. Daga cikin ire-iren karin da ke fitowa a sassan jiki, akwai wani kari da ake kira da ‘ganglion cyst’ a turance. Irin wannan kari, yawanci ya fi fitowa ne a kan gaba.

2- Girman kari, kan kasance kamar girman kwayar wake zuwa girman kwayar gurjiya. Sannan, yanayinsa idan aka taba ko aka latsa shi yana kama da balan-balan ko ‘yar mitsitsiyar kwallo cike da ruwa mai kauri. A dunkule dai, wannan kari bulli ne da ke dauke da wani ruwa mai yauki da kuma kauri a ciki.

  • Xi: Ya Kamata A Hada Hannu Domin Tafiyar Da Tattalin Arzikin Duniya Bisa Adalci Da Daidaito
  • CMG Da El Comercio Group Na Kasar Peru Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zurfafa Hadin Gwiwa

3- Abin farin ciki shi ne, wannan kari ba kansa ko daji ba ne. Don haka, babu fargabar cewa zai iya fantsama zuwa sassan jiki ko kuma ya tilasta yanke hannun.

4- Kashi tamanin da takwas cikin dari (88%) na wannan kari, na fitowa ne a kan gabar tsintsiyar hannu; kashi goma sha daya cikin dari (11%) kuma, yana fitowa ne a gabobin tafin sawu da idon sawu.

5- Har ila yau, kowa zai iya samun wannan kari, sai dai mata sun ninka maza sau uku wajen samun karin tsintsiyar hannu. Sannan kuma, kashi saba’in cikin dari (70%); yana faruwa ne tsakanin shekara 20 zuwa 40 na rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

6- Kashi sittin zuwa saba’in cikin dari (60 – 70%) na karin tsintsiyar hannu, na fitowa ne a bayan tsintsiyar hannu. Inda sauran kason kuma ke fitowa a gaban ko gefen tsintsiyar hannun.

7- Mene ke kawo wannan kari? Babu wani takamaiman sababi da ke kawo wannan kari. Sai dai, ana ganin bugu, kabar majinar gaba, tunzuri ga majina ko tantanin gaba; sakamakon ayyukan da ke bukatar maimaituwar motsin gabar tsintsiyar hannun na kara hadarin faruwarsa.

8- Alamomin karin tsintsiyar hannu: Daga cikin alamomin karin tsintsiyar hannu akwai:

i- Bayyanar bulli ko tudun karin; idan aka lankwashe gabar tsintsiyar hannu. Kuma karin a wuri guda yake, ba yawo yake yi ba.

  1. Karin yana girma ne kadan-kadan, zai iya bullowa kwatsam! A wani lokaci kuma, sai ya kankance ko ma ya bace bat. Haka kuma, zai iya dawowa a kowane irin lokaci.

iii. Mafi yawan lokaci, karin tsintsiyar hannu; ba ya yin ciwo, sannan kuma ba shi da wata matsala. Amma ya kan fara yin ciwo ne, idan karin ya fara shake ko danne jijiyar laka a hanyarta ta zuwa hannu. Haka nan, yayin da karin ya danne jijiyar laka; zai iya haifar da ciwo, zugi, rauni ko rashin kwarin wani yatsa ko yatsun hannu.

9- Yaushe ya kamata a tuntubi likita? Za a iya tuntubar likita ne da zarar karin ya fara haifar da alamun da muka ambata a sama, domin bin hanyoyin magance karin da suka hada da; zuke ruwan cikin karin tare da sanya maganin da zai kafar da ruwan karin. Haka nan, ana yin tiyata don cire karin daga tushensa da sauran hanyoyi.

Bugu da kari, likitocin fisiyo na taka rawar gani kafin da kuma bayan tiyatar; wajen magance matsalolin ciwo, raunin ko rashin kwarin yatsu ko hannu da kuma magance matsalar tabon tiyata da sauran makamantansu.

10- Har wa yau, imma karin ba ya ciwo amma ka damu da munin sifar da karin ya jawo maka; to kana iya zuwa asibiti domin a cire maka shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HandHannu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Next Post

Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Sasanta Batun Nukiliyar Iran A Siyasance

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

6 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

7 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

8 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

8 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

9 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

9 hours ago
Next Post
Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Sasanta Batun Nukiliyar Iran A Siyasance

Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Sasanta Batun Nukiliyar Iran A Siyasance

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.