• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyar Masu Jan Hankali Game Da Coci Mafi Dadewa A Birtaniya

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Al'ajabi
0
Abubuwa Biyar Masu Jan Hankali Game Da Coci Mafi Dadewa A Birtaniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ginin wanda aka yi shi da duwatsu a kusa da gabar Kogin Thames, yana bangaren dama da ginin Majalisar Dokokin Birtaniya a tsakiyar birnin Landan, Cocin Westminster Abbey ya kasance wani wurin shirya kasaitattun bukukuwan kasa masu alfarma cikin karni masu yawa.

Cocin ta kasance mai dimbin tarihi, inda ake nada sarakunan Birtaniya ciki har da bikin nadin Sarauniya da aka yi a shekarar 1953.

  • IAEA: Za A Tattauna Batun Hadin Gwiwa Tsakanin Amurka Da Birtaniya Da Australiya

Ginin wanda ake gani yanzu, an sake gina shi ne a zamanin Sarki Henry III, a 1245 to amma an gina ta ne tun a shekarar 960AD.

Dakta Hannah Boston, malama a Kwalejin Magdalen ta Jami’ar Odford ta ce ‘Ginin ya kasance wani wurin taron siyasa da mulkin Ingila na kusan dubban shekaru.

A yau fiye da fitattun mutane 3,300, wadanda suka hadar da sarakuna, sun kasasnec ko dai an binne su a ciki, ko kuma a shirya gawarwakinsu a cikin cocin Westminster Abbey.

Labarai Masu Nasaba

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

A yayin da miliyoyin mutane ke bankwanan karshe da gawar Sarauniya Elizabeth II a lokacin jana’izarta daga Cocin ta Westminster Abbey, ga wasu abubuwa biyar game da tsohon ginin.

1. An daura auren iyalan gidan Sarauta 16 a cikinta
A shekarar 2011, sanye da tufafi masu launin ruwan dorawa Sarauniya Elizabeth II, ta halarci daurin auren jikanta Yarima William da matarsa Kate Middleton, wanda shi ne aure na baya-bayan nan da aka daura a cocin.

Daurin auren Yariman ya biyo bayan jerin auren gidan sarautar da ake yi a cocin tun shekara 900 da suka gabata.

Kawo yanzu an daura aure 16 na iyalan gidan sarauta a cocin, tun daga kan auren Henry I, wanda ya auri Gimbiyar Scotland Matilda a shekarar 1100, da kuma auren Elizabeth lokacin tana Gimbiya tare da mijinta Yarima Philip a shekarar 1947.

2. Gidan da tsohuwar kofar Birtaniya take
A shekarar 2005 wani bincike ya gano cewa a Cocin Westminster Abbey ne tsohuwar kofar masarautar Birtaniya take.

An kera kofar ne a shekarun 1050, gabanin yakin Norman.
Dakta Boston ta ce Sarki Edward wanda ya yi zamani tsakanin shekarun 1042 1066, shi ne ya gina cocin.

To amma cikin abubuwan da aka gina cocin da su tun wancan lokaci, zuwa yanzu kofar ce kawai ta rage.

3. Makabartar manyan sarakuna, da wasu dubban mutane
Cocin Westminster Abbey ta kasance makabarta ga Sarakunan Birtaniya kusan 30, na farko shi ne Sarki Edward. Sauran sun hada da Sarauniya Elizabeth I, da Sarauniyar Scots, da kuma gimbiyoyi 11 (matayen Sarakuna masu ci) Sarki na karshe da aka binne a cocin shi ne Sarki George II a shekarar 1760, to amma ba sarakuna kadai ake binnewa a cocin ba.

An binne fitattun mutane fiye da mutum 3,300 a cocin, wadanda suka hada da Sir Isaac Newton, da Stephen Hawking, da George Frederic Handel da kuma marubuciyar wakokin nan Mary Trebor.

A nan ne kuma aka binne shahararrun mawaka da marubuta, kamar su Jane Austen da Charlotte, da Emily da kuma Anne Brontë.
Jana’iza ta baya-bayan nan da aka yi a cocin ita ce jana’izar Gimbiya Diana a shekarar 1997, sai kuma ta Sarauniya Elizabeth II da aka yi a yanzu.

4. Kujerar nadin sarauta
Ana yi wa kujerar nadin sarauta kallon daya daga cikin manya kuma fitattun kujeru a fadin duniya, kuma ta kasance a cikin wannan gini tsawon karni bakwai.
Sarki Edward I ne ya kera kujerar daga wani fitaccen dutse mai dimbin tarihi da ya dauko daga yankin Scotland.

Sarauniya Elizabeth II ta zauna a kan kujera da aka ajiye kan dutsen yayin bikin nadinta a shekarar 1953, haka kuma za a sake fito da kujerar a yayin bikin nadin sabon sarki Charles lll.

Tun shekarar 1066, duka sarakunan da aka nada in ban da guda biyu an nada su ne a cocin Westminster Abbey, inda ka nada sarakuna 39.

5. Wurin tarihi ne na hukumar kula da al’adu da tarihi na Majalisar Dinkin Duniya, kuma wasu taswirar gine-ginensa na hasashen karshen duniya
An kawata gaban saman ginin cocin da jerin kananan gumaka masu ruwan zinari, wadanda suke uku daga cikinsu ke hasahen lokacin tashin duniya.

An gina su ne da wasu kanana-kananan duwatsu masu launin ruwan gilashi da ke dauke da launuka masu yawa, wadanda aka yanka zuwa suffofi daban-daban.

Gumakan wadanda ake kira da gumakan Cosmati, suna hasashen cewa duniya za ta wanzu zuwa shekara 19,683.
A baya-bayan nan ne dai sakon da wadannan gumaka ke dauke da shi ya bayyana ga mutane, bayan da aka yi wa ginin cocin kwaskwarima inda aka kawar da wasu abubuwan da a baya suka rufe wannan sako.

A shekarar 1987 wadannan gumaka da tsohuwar kofa, tare da kujerar sarautar suka zama wasu abubuwa masu muhimmanci da al’adun duniya, a lokacin da aka lissafa fadar Westminster da cocin Westminster Abbey, cikin kayayyakin hukumar UNESCO.
Mun ciro muku daga BBC.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Gabon

Next Post

Wang Yi Ya Halarci Muhawarar Babban Taron MDD Karo Na 77

Related

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

1 month ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

2 months ago
Yadda Rashin ÆŠaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya ÆŠauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin ÆŠaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya ÆŠauke Shi

3 months ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

3 months ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

3 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri FyaÉ—e A Bauchi

4 months ago
Next Post
Wang Yi Ya Halarci Muhawarar Babban Taron MDD Karo Na 77

Wang Yi Ya Halarci Muhawarar Babban Taron MDD Karo Na 77

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara

August 14, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato

’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato

August 14, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

August 14, 2025
An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

August 14, 2025
Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

August 14, 2025
Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

August 14, 2025
Allah Zai Kunyata Masu ÆŠaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu ÆŠaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu

August 14, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.