Gwamnatin jihar Adamawa ta amince da biyan mafi karancin albashi na Naira 70,000 ga ma’aikatan kananan hukumomi a fadin jihar.
Kwamishinan yada labarai a jihar, Mista Iliya James ne ya bayyana hakan bayan kammala taron majalisar zartarwa (SEC) ta jihar a ranar Laraba a Yola, babban birnin jihar.
- Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci
- An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda
Taron Majalisar, wanda Gwamna Ahmadu Fintiri ya jagoranta, ya yi bitar karshe na kasafin kudin shekarar 2024, inda ya nuna cewa, an samu gagarumin ci gaba na kashi 80 cikin 100 na ayyukan da aka yi idan aka kwatanta da kashi 56 cikin 100 na shekarar 2023.
A nasu jawabin, kwamishinonin kudi da kasafin kudi Misis Augustina Wandamiya da Mista Emanuel Pridimso sun bayyana cewa, an yi bitar kasafin ne da nufin gano wuraren da aka samu rarar kudi da kuma tabbatar da cewa, an kashe kudin kasafin shekarar 2024 a inda ya dace.
Sun kara da cewa, jihar ta kula da tsari wajen aiwatar da kasafin kudi, tare da tabbatar da gaskiya, wanda hakan, ya taimaka wajen samar da kyakkyawan aiki a ayyukan raya jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp