• English
  • Business News
Monday, September 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

by Sulaiman
3 hours ago
in Ra'ayi Riga
0
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shi dai harshe wani tsari ne ga bil adam wanda ake amfani da shi wajen isar da sako ko musayar bayanai tsakanin juna. Harshe ya kunshi sauti da rubutu a matsayin wani bangare na al’adun wata kabila. Harshen ya bambanta tsakanin wannan al’umma zuwa waccan al’umma.

Harshen Mandarin, dadadden harshe ne mai dogon tarihi da al’ummar Sinawa ke amfani da shi, ya kasance harshen da aka fi amfani da shi a duniya. Yau an wayi gari harshen Mandarin yana yaduwa cikin sauri a nahiyar Afrika. Sakamakon bunkasuwar ma’amalar cinikayya, diplomasiyya da musayar al’adu tsakanin Sin da Afirka ya sanya harshen Mandarin ya samu karbuwa a matsayin wata hanyar da za ta saukaka mu’amala da kuma zurfafa dangantaka a fannoni daban daban tsakanin al’ummomin Afirka da na Sin.

Bugu da kari harshen Mandarin abu ne mai muhimmancin gaske ga ’yan kasuwar Afirka da suke mu’amala da ’yan kasuwar Sin, abin da zai saukaka masu dawainiya da masu yi masu tafinta yayin da suke tattaunawa tsakaninsu da abokan cinikayya na kasar Sin. Harshen Mandarin ya bude damammaki ga jama’a tare da samar da aikin yi, musamman idan aka yi la’akari da yadda a kullum bukatar masu iya magana da Mandarin ke karuwa.

Har wa yau kuma, yaduwar harshen na Mandarin yana da alfanu wajen fahimtar al’adun kasar Sin, abin da zai taimaka wajen wayar da kan masu korafi kan batun ’yancin dan adam, tare da fahimtar yadda Sin ke samun bunkasuwa cikin sauri.

Idan muka duba a fannin ilimi da al’adu kuwa, kasar ta Sin ta rubanya yawan gurabun karo ilimi ga dubban dalibai daga Afirka, abin da ya sanya koyon harshen na Mandarin ya zama wajibi ga irin wadannan dalibai.

Labarai Masu Nasaba

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

Yanzu haka dai akwai jami’o’i da kwalejoji da cibiyoyi da dama da ake koyar da harshen mandarin a kasashen Afirka. Yayin da dalibai masu koyon harshen Mandarin suke ta karuwa a kullum. Misali a kasar Uganda akwai cibiyar koyar da harshen Mandarin wadda ta fara da dalibai 30 a shekara goma da ta gabata, amma a yau tana da sama da dalibai 400.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zulum Ya Rabawa Talakawan Dikwa  Tallafin Kuɗi Da Abinci

Next Post

NAF Ta Fatattaki ‘Yan Ta’addan Da Suka Addabi Al’ummar Jihar Kwara

Related

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

2 days ago
Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

4 days ago
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Ra'ayi Riga

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

1 week ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

2 weeks ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

2 weeks ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

3 weeks ago
Next Post
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

NAF Ta Fatattaki 'Yan Ta'addan Da Suka Addabi Al'ummar Jihar Kwara

LABARAI MASU NASABA

ASUU

Ƙungiyar ASUU Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwanaki 14 Ta Biya Buƙatunta 

September 29, 2025
Xi: Ya Kamata A Sa Kaimi Ga Dunkulewar Addinan Sin Da Kyawawan Al’adun Gargajiya Na Kasar

Xi: Ya Kamata A Sa Kaimi Ga Dunkulewar Addinan Sin Da Kyawawan Al’adun Gargajiya Na Kasar

September 29, 2025
Za A Kira Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin Jam’Iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Na 20

Za A Kira Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin Jam’Iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Na 20

September 29, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

NAF Ta Fatattaki ‘Yan Ta’addan Da Suka Addabi Al’ummar Jihar Kwara

September 29, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Zulum Ya Rabawa Talakawan Dikwa  Tallafin Kuɗi Da Abinci

Zulum Ya Rabawa Talakawan Dikwa  Tallafin Kuɗi Da Abinci

September 29, 2025
Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

September 29, 2025
Yadda Ganduje Ya Janye Hannun Jarin Jihar Kano, Ya Saka Ƴaƴansa 3 A Dala Inland Dry Port

Yadda Ganduje Ya Janye Hannun Jarin Jihar Kano, Ya Saka Ƴaƴansa 3 A Dala Inland Dry Port

September 29, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna Zai Dawo Aiki 1 Ga Oktoba – NRC

Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna Zai Dawo Aiki 1 Ga Oktoba – NRC

September 29, 2025
Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad

Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad

September 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.