• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’ummar Kasashen Turai Na Dandana Kudar Rikicin Rasha Da Ukraine

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Al’ummar Kasashen Turai Na Dandana Kudar Rikicin Rasha Da Ukraine
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau kusan watanni shida ke nan, tun bayan barkewar rikici a tsakanin Rasha da Ukraine. Sakamakon rikicin, kamfanonin samar da makamai da na hatsi na Amurka sun ci kazamar riba, a yayin da kamfanonin samar da makamashi ma ba su so a bar su a baya. 

Bayanai na nuna cewa, sakamakon yadda kasashen Turai suka biyewa kasar Amurka wajen kakaba takunkumai kan Rasha, yanzu haka, kasashen Turai da dama na fuskantar matsalar karancin makamashi mai muni, hakan ya tilasta musu sayen iskar gas daga wajen Amurka a kan farashi mai tsada, matakin da ya sa kamfanonin samar da makamashi na kasar Amurka cin kazamar riba, inda kusan kowane jirgin dakon iskar gas na kamfanonin Amurka da ke zuwa Turai, na iya cin kazamar ribar da ta kai dala miliyan 100.

  • Ma’aikatan Gwamnati Sun Fi ‘Yan Siyasa Cin Hanci Da Rashawa – Kwamitin Majalisar Dattawa

Abin takaici shi ne, a yayin da ake fuskantar hauhawar farashin wutar lantarki da yadda aka kayyade wutar da ake samar musu, al’ummar kasashen Turai su ne suke dandana kudar rikicin.

Kwanan nan ne, zanga zanga ta barke a birnin Prague, babban birnin kasar Czech, inda kimanin mutane dubu 70 suka bazama kan tituna suna kira ga gwamnati da ta dauki matakai na shawo kan saurin hauhawar farashin makamashi, tare da sukan gwamnati a kan manufarta ta yin biyayya ga kasashen yammaci wadda ta illata moriyar kasar.

Kwanan baya, shugaban kasar Amurka Joe Biden, ya sake sanar da samar da gudummawar soji da za ta kai darajar kusan dala biliyan 3 ga kasar Ukraine.

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Kafin wannan, Amurkar ta samar da gudummawar soji a kalla dala biliyan 10.6 ga Ukraine. Kamar yadda tsohon dan majalisar dokokin kasar Burtaniya, George Galloway ya fada ne, “Kamar dai yadda Amurka ke son ganin Ukraine ta yi ta yaki har sai a karshe ta fadi kasa warwas, haka ta shirya ganin durkushewar Turai.”

Amurka dai ta tada rikicin tsakanin Rasha da Ukraine, ta kuma rika rura wutar rikicin, amma ta koma gyefe tana cin riba a fakaice. Nan ba da dadewa ba, za a shiga lokacin hunturu a Turai, amma ko kasashen Turai za su ci gaba da dandana kudar sakamakon rikicin? (Mai Zane:Mustapha Bulama)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Zargin Budurwa Da Kashe Mahaifiyar Saurayinta Da Adda A Kamaru

Next Post

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Zababben Shugaban Kenya

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

4 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

5 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

6 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

7 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

8 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

9 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Zababben Shugaban Kenya

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Zababben Shugaban Kenya

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.