A ’yan kwanakin da suka wuce, shugaban tawagar jami’an lafiya ta kasar Sin a kasar Tanzania, Zhang Junqiao ya rasu, a kokarinsa na ceto wata mata da ta fada cikin teku a Dar es Salaam. Yayin taron manema labarai na yau Talata, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun, ya ce Zhang Junqiao ya yi jarumta wajen sadaukar da ransa domin ceton rai da nuna ruhin abotar dake tsakanin Sin da Afrika a aikace. Kakakin ya kuma mika ta’aziyya ga iyalan Zhang Junqiao da alhinin rashin hazikin mamban na tawagar jami’an lafiya ta Sin a Afrika.
Ya kara da cewa daga shekarar 1963 zuwa yanzu, an shafe shekaru 62 Sin tana bayar da tallafin kiwon lafiya a nahiyar Afrika, kuma tarihin tawagar ta Sin a Tanzania ya kai shekaru 58. Ya ce jami’an sun nuna halin kirki wajen kula da jama’ar kasar, haka kuma sun kafa wata tawagar jami’an lafiya da ba za a iya rusa ta ba. Ya ce tarihi da al’ummun Sin da Afrika, ba za su taba mantawa da gudunmuwar tawagar ga abotar dake tsakanin Sin da Afrika ba. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp