• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfanin Zogale 18 Ga Lafiyar Jikin Dan’adam

by Sani Anwar and Sulaiman
12 months ago
in Kiwon Lafiya
0
Amfanin Zogale 18 Ga Lafiyar Jikin Dan’adam
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana harkokin lafiyar abinci, sun bayyana amfanin da ganyen zogale ke da shi a jikin Dan’adam, sakamakon sinadarin da yake kunshe da su.

Har ila yau, bincike ya tabbatar da cewa; zogale itace ne mai matukar albarka, domin kuwa ya kan fito har a wurin da babu ruwa.

Don haka, ganyensa da sassakensa; na da matukar amfani a jikin mutum. Sannan kuma, yana da dauke da sinadarin A.B.C.D har ma da E, kana kuma yana dauke da sinadarin calcium da potassium, kana kuma mansa yana cikin mayukan da suka fi tsada a duniya.

Kazalika, akwai magunguna 18 da zogale ke yi ga lafiyar Dan’adam kamar haka:

– Ana dafa ganyen zogale da zuma a sha kamar shayi, domin maganin Olsa (Ulcer).

Labarai Masu Nasaba

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

– Ana kuma shafa danyen ganyen zogale a kan goshi, don maganin ciwon kai.

– Haka nan, ga wanda ya ji wani rauni ko sara; idan ya shafa danyen ganyen zogale, jinin zai tsaya nan take da izinin Allah.

– Ga mai fama da kurajen jiki, sai ya hada garin zogale da man zaitun; ya rika shawa.

– Ana kuma zuba garin zogale a kan gyambo ko wani rauni, domin ya yi saurin warke.

– Sanya garin zogale a cikin abinci, na maganin hawan jini da kuma kara wa mutum kuzari,

– Ana dafa ganyen zogale, a saka kanwa ‘yar kadan; don maganin shawara.

– Ga mai fama da ciwon ido, zai rika diga ruwan danyen zogale; haka nan shi mai fama da ciwon kunne.

– Macen da ke shayarwa kuma, ta dafa furen zogale da zuma; domin samun karin yawan ruwan nono.

– Wanda ke fama da yawan fitsari ko ciwon Siga, sai ya rika shan furen zogale da citta kamar shayi.

– Kazalika, cin zogalen ma a haka; na maganin tsutsar ciki, musamman ga yara.

– Ana daka ganyen zogale da ‘ya’yan baure a sha da nono ko kunu, domin kuwa yana maganin ciwon hanta.

– Ga mai fama da sanyin kashi ko wani kumburi, sai ya soya ‘ya’yan zogale ya daka su; ya kuma hada da man kwakwa (man- ja) sai ya rika shafawa.

– A daka zangarniyar zogale da ‘ya’yan da ke ciki da kaninfari, citta, masoro da kuma kimba, domin karin karfin namiji, sannan yana kara wa mata nishadi.

– A daka saiwar zogale da ‘ya’yan kankana a sha a nono, yana maganin tsakuwar ciki (Apendis).

– Haka nan, yana maganin typhoid, maleriya, basir da shawara; ta hanyar yawan shan ruwan dafaffen zogale.

– Kazalika, zogale na rage radadin ciwon HIB ta hanyar shan dafaffen ruwan zogalen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dole Matasanmu Su Rungumi Kasuwanci Na Zamani – Firdausi Dahiru

Next Post

Ƙungiyar Malamai Ta Ƙasa Ta Karrama Gwamna Yusuf Da Lambar Yabo

Related

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

1 week ago
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi
Kiwon Lafiya

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

1 week ago
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Kiwon Lafiya

Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

2 weeks ago
Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya
Kiwon Lafiya

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

1 month ago
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu
Kiwon Lafiya

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

1 month ago
Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati
Kiwon Lafiya

Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati

2 months ago
Next Post
Ƙungiyar Malamai Ta Ƙasa Ta Karrama Gwamna Yusuf Da Lambar Yabo

Ƙungiyar Malamai Ta Ƙasa Ta Karrama Gwamna Yusuf Da Lambar Yabo

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.