• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfanin Zogale 18 Ga Lafiyar Jikin Dan’adam

by Sani Anwar and Sulaiman
10 months ago
in Kiwon Lafiya
0
Amfanin Zogale 18 Ga Lafiyar Jikin Dan’adam
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana harkokin lafiyar abinci, sun bayyana amfanin da ganyen zogale ke da shi a jikin Dan’adam, sakamakon sinadarin da yake kunshe da su.

Har ila yau, bincike ya tabbatar da cewa; zogale itace ne mai matukar albarka, domin kuwa ya kan fito har a wurin da babu ruwa.

Don haka, ganyensa da sassakensa; na da matukar amfani a jikin mutum. Sannan kuma, yana da dauke da sinadarin A.B.C.D har ma da E, kana kuma yana dauke da sinadarin calcium da potassium, kana kuma mansa yana cikin mayukan da suka fi tsada a duniya.

Kazalika, akwai magunguna 18 da zogale ke yi ga lafiyar Dan’adam kamar haka:

– Ana dafa ganyen zogale da zuma a sha kamar shayi, domin maganin Olsa (Ulcer).

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati

Yadda Hadarin Mutuwa Ke Karuwa Yayin Ko Bayan Saduwa Da Iyali

– Ana kuma shafa danyen ganyen zogale a kan goshi, don maganin ciwon kai.

– Haka nan, ga wanda ya ji wani rauni ko sara; idan ya shafa danyen ganyen zogale, jinin zai tsaya nan take da izinin Allah.

– Ga mai fama da kurajen jiki, sai ya hada garin zogale da man zaitun; ya rika shawa.

– Ana kuma zuba garin zogale a kan gyambo ko wani rauni, domin ya yi saurin warke.

– Sanya garin zogale a cikin abinci, na maganin hawan jini da kuma kara wa mutum kuzari,

– Ana dafa ganyen zogale, a saka kanwa ‘yar kadan; don maganin shawara.

– Ga mai fama da ciwon ido, zai rika diga ruwan danyen zogale; haka nan shi mai fama da ciwon kunne.

– Macen da ke shayarwa kuma, ta dafa furen zogale da zuma; domin samun karin yawan ruwan nono.

– Wanda ke fama da yawan fitsari ko ciwon Siga, sai ya rika shan furen zogale da citta kamar shayi.

– Kazalika, cin zogalen ma a haka; na maganin tsutsar ciki, musamman ga yara.

– Ana daka ganyen zogale da ‘ya’yan baure a sha da nono ko kunu, domin kuwa yana maganin ciwon hanta.

– Ga mai fama da sanyin kashi ko wani kumburi, sai ya soya ‘ya’yan zogale ya daka su; ya kuma hada da man kwakwa (man- ja) sai ya rika shafawa.

– A daka zangarniyar zogale da ‘ya’yan da ke ciki da kaninfari, citta, masoro da kuma kimba, domin karin karfin namiji, sannan yana kara wa mata nishadi.

– A daka saiwar zogale da ‘ya’yan kankana a sha a nono, yana maganin tsakuwar ciki (Apendis).

– Haka nan, yana maganin typhoid, maleriya, basir da shawara; ta hanyar yawan shan ruwan dafaffen zogale.

– Kazalika, zogale na rage radadin ciwon HIB ta hanyar shan dafaffen ruwan zogalen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dole Matasanmu Su Rungumi Kasuwanci Na Zamani – Firdausi Dahiru

Next Post

Ƙungiyar Malamai Ta Ƙasa Ta Karrama Gwamna Yusuf Da Lambar Yabo

Related

Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati
Kiwon Lafiya

Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati

1 day ago
Kwanciyar Aure
Kiwon Lafiya

Yadda Hadarin Mutuwa Ke Karuwa Yayin Ko Bayan Saduwa Da Iyali

1 week ago
Dalilin Ciwon Baya Yayin Goyon Ciki Da Hanyar Magance Shi
Kiwon Lafiya

Dalilin Ciwon Baya Yayin Goyon Ciki Da Hanyar Magance Shi

2 weeks ago
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
Kiwon Lafiya

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

4 weeks ago
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

4 weeks ago
Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 
Kiwon Lafiya

Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 

1 month ago
Next Post
Ƙungiyar Malamai Ta Ƙasa Ta Karrama Gwamna Yusuf Da Lambar Yabo

Ƙungiyar Malamai Ta Ƙasa Ta Karrama Gwamna Yusuf Da Lambar Yabo

LABARAI MASU NASABA

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

August 2, 2025
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.