• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka, Kasar Da Ke Kawo Cikas Ga Kokarin Duniya Na Shawo Kan Annobar Covid-19

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka, Kasar Da Ke Kawo Cikas Ga Kokarin Duniya Na Shawo Kan Annobar Covid-19
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Annobar Covid-19 matsala ce da ke addabar duniya baki daya, wadda ke bukatar hadin gwiwar kasa da kasa don shawo kanta. Sai dai abin takaici shi ne, cikin shekaru uku da suka wuce, kasancewarta babbar kasa mafi karfi a duniya, Amurka ta yi ta kawo cikas ga kokarin kasa da kasa na shawo kan cutar, a maimakon daukar nauyin da ke rataye a wuyanta.

A matsayinta na kasa mai ci gaban aikin kiwon lafiya a duniya, mahukuntan kasar ta Amurka ba su dauki matakan da suka kamata ba na tinkarar annobar, inda suka yi biris da lafiyar al’umma da rayukansu, kuma a maimakon haka, sai suka mai da hankali a kan siyasantar da annobar, matakin da ya sabbaba saurin yaduwar annobar.

  • Shugaba Talon Na Benin Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin

A cikin shekarun uku da suka wuce, an samu yaduwar kusan dukkanin nau’o’in cutar Covid-19 a kasar, inda sama da ’yan kasar miliyan 100 suka harbu da cutar, baya ga kuma sama da miliyan daya da suka rasa rayukansu. Ban da haka, gwamnatin kasar ba ta dauki mataki na kayyade harkokin fita daga kasar ba, inda ta bar cutar ta rika yaduwa zuwa sauran sassan duniya.

Alkaluman da aka samar sun yi nuni da cewa, daga watan Afrilun shekarar 2020 zuwa watan Maris na shekarar 2021, gaba daya al’ummar kasar miliyan 23 da dubu 195 suka fice daga kasar, wadanda suka tafi sassa daban daban na duniya. Sa’an nan, yadda kasar ta tilastawa bakin haure da su koma kasashensu na asali ba tare da lura da yanayin lafiyarsu ba, ya kara tsananta yanayin annobar da kasashen Latin Amurka ke ciki.

A yayin da duniya ke kokarin shawo kan annobar, kasar Amurka ta kuma fice daga hukumar lafiya, baya ga tara dimbin rigakafin cutar a gida, ba tare da raba su ga sauran kasashe masu bukata ba. Alkaluman da cibiyar kandagarkin cututtuka ta Amurka ta samar sun shaida cewa, daga watan Maris zuwa watan Satumban shekarar 2021, Amurkar ta bata a kalla rigakafi miliyan 15.1. Idan ba a manta ba, Amurka ta tura rigakafin da lokacin aikinsa ya kusan karewa zuwa kasashen Afirka, matakin da ya jawo suka daga kasashen.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

In mun waiwayi tarihi, sau tari mabambantan annoba sun haifar da munanan hasarori ga ’yan Adam, kuma tarihi ya shaida cewa, cuta ba ta san iyaka ko kabila ba. Shekaru ukun da suka wuce da ake yaki da cutar Covid-19 ma sun shaida mana cewa, ’yan Adam makomarsu daya ce, kuma siyasantar da annobar ba zai haifar da komai ba illa lalata hadin gwiwar kasa da kasa wajen dakile cutar, tare da haifar da karin hasarori ga al’ummar duniya. (Mai Zane: Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Amurka Wadda Ta Fi Yada Cutar COVID-19 Ta Bayyana Alkalumanta Kan Yanayin Yaduwar Cutar

Next Post

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 A Neja, Sun Kwace Makamai

Related

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

13 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

14 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

15 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

16 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

17 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 A Neja, Sun Kwace Makamai

'Yansanda Sun Kashe 'Yan Bindiga 4 A Neja, Sun Kwace Makamai

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.