• English
  • Business News
Monday, June 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ta Daba Wa Kanta Wuka Bisa Karin Harajin Da Ta Yi 

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka Ta Daba Wa Kanta Wuka Bisa Karin Harajin Da Ta Yi 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce zai sanar da karbar harajin kwastam na ramuwar gayya kan kayayyakin kasashe daban daban, a yau Laraba, a matsayin wani sabon mataki karkashin yunkurinsa na ta da “yakin harajin kwastam” a duniya. Matakin da shugaba Trump ke son dauka ya janyo damuwa a duniya. Kamar yadda wani masanin al’amuran duniya dan kasar Kenya mai suna Adhere Cavince ya fada, “Manufar kasar Amurka ta zama shingen hana farfadowar tattalin arzikin duniya, da ci gaban kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka.”

Amurka tana kallon kanta a matsayin mai tafka hasara a cinikayyar duniya, lamarin da ya hana ta damar raya masana’antu a cikin gidanta. Kana ta hanyar karbar karin harajin kwastam kan kayayyakin da ake shigowa da su cikin kasar daga ketare, za ta iya daidaita matsalar da take fuskanta. Sai dai ko gaskiya ne haka batun yake?

  • Tinubu Ya Tafi Faransa Ziyarar Aiki Na Mako 2
  • Tinubu Ya Kori Mele Kyari, Ya Naɗa Ojulari A Matsayin Shugaban NNPC

Hakika, dangane da batun, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi magana mai ma’ana a kwanan nan, yayin ziyararsa a kasar Rasha. Ministan ya ce, duk wata kasa na iya gamuwa da wasu matsaloli, amma ya kamata a dogara da kai wajen neman mafita, maimakon dora laifi kan sauran kasashe. Amurka na son ganin sauran kasashe suna biyanta kudi, don kawai daidaita matsalolinta na kashin kanta da take fuskanta. Sam ba za ta samu biyan bukata ba. Kana manufarta za ta lalata muhallin raya tattalin arzikin duniya, da girgiza imanin da ake da shi kan kasar.

A ganin Shen Yi, farfesa mai nazarin ilimin al’amuran siyasa na duniya, dake aiki a jami’ar Fudan ta kasar Sin, manufar kasar Amurka ta karbar karin haraji ba za ta haifar da da mai ido ba. A cewarsa, idan kowace kasa ta yi wa kasar Amurka ramuwar gayya, kana ba su canza manufofinsu kan sauran kasashe ba, to, za a iya ganin canzawar yanayin kasuwanci a duniya, amma ba tare da samun “farfadowar kasar Amurka” ba. Za a maye gurbin kasuwannin kasar Amurka da na sauran kasashe da yankuna, lamarin da zai mai da Amurka saniyar ware. Cikin dogon wa’adi, jama’ar kasar Amurka za su tafka mafi yawan hasara, kana mutanen duniya za su fara ganin wani sabon yanayin da kasar Amurka da ba ta iya babakere a duniya.

Kana a nahiyar Afirka ma ana samun ra’ayin da ya yi kama da ra’ayin farfesa Shen. Misali, shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama, a kwanan baya ya taba bayyana cewa, matakin Amurka na karbar karin harajin kwastam zai karfafa kasashen nahiyar Afirka su gaggauta tsayawa da kafafuwansu. A ganin shugaban, kasashen Afirka suna dogaro kan wata hanyar tsarin ciniki da ta hada su da kasashen Turai, wadda aka kafa tun daga lokacin mulkin mallaka. Sai dai wannan tsari ya haifar da illa ga cinikin nahiyar Afirka, saboda har yanzu ba a samu ciniki sosai tsakanin kasashen dake nahiyar ba. Amma sabon matakin kasar Amurka zai sa nahiyar Afirka kara dogaro da kai, da yin karin ciniki a tsakanin mabambantan kasashe dake nahiyar Afirka.

Labarai Masu Nasaba

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

Sanin kowa ne, ciniki mai inganci na bukatar kasuwa mai ‘yanci, da takarar da ake yi cikin daidaito, gami da manufa mai dorewa. Idan kasar Amurka ta ki samar da wadannan abubuwa, to, babu wani abun da za a yi, in ban da mai da kasar saniyar ware, da kara tabbatar da hadin kai tare da sauran abokan hulda. (Bello Wang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Janar Tsiga Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Bayan Shafe Kwanaki 56 A Hannun ‘Yan Bindiga 

Next Post

Sabbin Motocin Bas 100 Masu Aiki Da Lantarki Sun Fara Jigilar Fasinjoji A Birnin Addis Ababa

Related

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

8 hours ago
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya
Daga Birnin Sin

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

9 hours ago
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

11 hours ago
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

12 hours ago
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

1 day ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

1 day ago
Next Post
Sabbin Motocin Bas 100 Masu Aiki Da Lantarki Sun Fara Jigilar Fasinjoji A Birnin Addis Ababa

Sabbin Motocin Bas 100 Masu Aiki Da Lantarki Sun Fara Jigilar Fasinjoji A Birnin Addis Ababa

LABARAI MASU NASABA

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

June 8, 2025
Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

June 8, 2025
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

June 8, 2025
Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

June 8, 2025
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.