• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ta Daba Wa Kanta Wuka Bisa Karin Harajin Da Ta Yi 

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 month ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka Ta Daba Wa Kanta Wuka Bisa Karin Harajin Da Ta Yi 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce zai sanar da karbar harajin kwastam na ramuwar gayya kan kayayyakin kasashe daban daban, a yau Laraba, a matsayin wani sabon mataki karkashin yunkurinsa na ta da “yakin harajin kwastam” a duniya. Matakin da shugaba Trump ke son dauka ya janyo damuwa a duniya. Kamar yadda wani masanin al’amuran duniya dan kasar Kenya mai suna Adhere Cavince ya fada, “Manufar kasar Amurka ta zama shingen hana farfadowar tattalin arzikin duniya, da ci gaban kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka.”

Amurka tana kallon kanta a matsayin mai tafka hasara a cinikayyar duniya, lamarin da ya hana ta damar raya masana’antu a cikin gidanta. Kana ta hanyar karbar karin harajin kwastam kan kayayyakin da ake shigowa da su cikin kasar daga ketare, za ta iya daidaita matsalar da take fuskanta. Sai dai ko gaskiya ne haka batun yake?

  • Tinubu Ya Tafi Faransa Ziyarar Aiki Na Mako 2
  • Tinubu Ya Kori Mele Kyari, Ya Naɗa Ojulari A Matsayin Shugaban NNPC

Hakika, dangane da batun, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi magana mai ma’ana a kwanan nan, yayin ziyararsa a kasar Rasha. Ministan ya ce, duk wata kasa na iya gamuwa da wasu matsaloli, amma ya kamata a dogara da kai wajen neman mafita, maimakon dora laifi kan sauran kasashe. Amurka na son ganin sauran kasashe suna biyanta kudi, don kawai daidaita matsalolinta na kashin kanta da take fuskanta. Sam ba za ta samu biyan bukata ba. Kana manufarta za ta lalata muhallin raya tattalin arzikin duniya, da girgiza imanin da ake da shi kan kasar.

A ganin Shen Yi, farfesa mai nazarin ilimin al’amuran siyasa na duniya, dake aiki a jami’ar Fudan ta kasar Sin, manufar kasar Amurka ta karbar karin haraji ba za ta haifar da da mai ido ba. A cewarsa, idan kowace kasa ta yi wa kasar Amurka ramuwar gayya, kana ba su canza manufofinsu kan sauran kasashe ba, to, za a iya ganin canzawar yanayin kasuwanci a duniya, amma ba tare da samun “farfadowar kasar Amurka” ba. Za a maye gurbin kasuwannin kasar Amurka da na sauran kasashe da yankuna, lamarin da zai mai da Amurka saniyar ware. Cikin dogon wa’adi, jama’ar kasar Amurka za su tafka mafi yawan hasara, kana mutanen duniya za su fara ganin wani sabon yanayin da kasar Amurka da ba ta iya babakere a duniya.

Kana a nahiyar Afirka ma ana samun ra’ayin da ya yi kama da ra’ayin farfesa Shen. Misali, shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama, a kwanan baya ya taba bayyana cewa, matakin Amurka na karbar karin harajin kwastam zai karfafa kasashen nahiyar Afirka su gaggauta tsayawa da kafafuwansu. A ganin shugaban, kasashen Afirka suna dogaro kan wata hanyar tsarin ciniki da ta hada su da kasashen Turai, wadda aka kafa tun daga lokacin mulkin mallaka. Sai dai wannan tsari ya haifar da illa ga cinikin nahiyar Afirka, saboda har yanzu ba a samu ciniki sosai tsakanin kasashen dake nahiyar ba. Amma sabon matakin kasar Amurka zai sa nahiyar Afirka kara dogaro da kai, da yin karin ciniki a tsakanin mabambantan kasashe dake nahiyar Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Sanin kowa ne, ciniki mai inganci na bukatar kasuwa mai ‘yanci, da takarar da ake yi cikin daidaito, gami da manufa mai dorewa. Idan kasar Amurka ta ki samar da wadannan abubuwa, to, babu wani abun da za a yi, in ban da mai da kasar saniyar ware, da kara tabbatar da hadin kai tare da sauran abokan hulda. (Bello Wang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Janar Tsiga Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Bayan Shafe Kwanaki 56 A Hannun ‘Yan Bindiga 

Next Post

Sabbin Motocin Bas 100 Masu Aiki Da Lantarki Sun Fara Jigilar Fasinjoji A Birnin Addis Ababa

Related

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal
Daga Birnin Sin

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

18 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

19 hours ago
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU
Daga Birnin Sin

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

21 hours ago
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

22 hours ago
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

23 hours ago
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

23 hours ago
Next Post
Sabbin Motocin Bas 100 Masu Aiki Da Lantarki Sun Fara Jigilar Fasinjoji A Birnin Addis Ababa

Sabbin Motocin Bas 100 Masu Aiki Da Lantarki Sun Fara Jigilar Fasinjoji A Birnin Addis Ababa

LABARAI MASU NASABA

Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

May 17, 2025
Dalilin Ƴansandan Kano Na Tsare Wasu Awaki

Dalilin Ƴansandan Kano Na Tsare Wasu Awaki

May 17, 2025
Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

May 17, 2025
Me Ya Sa Manchester United Ta Fi Yin Kokari A Europa League?

Me Ya Sa Manchester United Ta Fi Yin Kokari A Europa League?

May 17, 2025
Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

May 17, 2025
Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa

Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa

May 17, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

May 17, 2025
Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya

Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya

May 17, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

May 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

May 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.