• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Aike Ɗan Shekara 67 Gidan Yari Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Mata 2 Fyaɗe Yana Ba Su ₦500 A Bauchi

by Muhammad
1 year ago
Bauchi

Ƴansanda a jihar Bauchi sun kama wani mutum mai suna, Bala Mohammed, ɗan shekara 67 kan zargin yi wa wasu ‘yan mata biyu fyaɗe a jihar Bauchi bayan ya yi musu roman baka kan zai ba kowacce daga cikinsu da kuɗi N500.

LEADERSHIP HAUSA ta samu labarin cewa, Bala yana amfani da dabarunsa ya yi wa ‘yan mata fyade, wanda wannan shi ne kusan karo na biyar kafin wannan.

Kakakin Rundunar ƴansandan Jihar Bauchi, Ahmed Wakil, ya ce, iyayen yaran da abin ya shafa sun shigar da kara kan Bala Mohammed kan zargin yi wa yaran su fyaɗe.

  • Ana Zargin Wani Hadimin ‘Yar Majalisa Da Yi Wa Almajiri Fyade A Kaduna
  • Masu Fyade Da ’Yan Luwadi 369 Aka Kama A 2023 A Katsina

“A ranar 22 ga watan Yunin 2024 da misalin, wani mai suna, Abubakar Danladi ɗan shekara 43 da Umar Ismail mai shekaru 65 daga Unguwar Mahaukata ta jihar Bauchi, sun kai rahoto hedikwatar ‘yansanda ta ‘A’, cewa Bala Mohammed mai shekaru 67 sun kama shi yana lalata da ‘ya’yansu mata da wata da aka laƙana wa suna Safiya (ba sunan gaskiya ba) mai shekaru 17 da Hassana (ba sunan gaskiya ba ne) me shekaru 16 duk masu adireshi ɗaya, kan ya shigar da su dakinsa yana lalata da su kan Naira dari biyar (N500) tsawon kwanaki biyar.

“Lokacin da ake yi wa wanda ake zargi tambayoyi, ya amsa aikata laifin,” cewr sanarwar.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Wakil ya ce har yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike, inda daga nan ne za a bayyana wanda ake zargin sannan a gurfanar da shi a gaban kotu domin gurfanar da shi gaban kuliya.

A wani labarin makamancin wannan, Kakakin ‘Yansandan Bauchi, Wakili ya ce wani suna Suleiman Musa, mai shekaru 28, ya lalata wata yarinya ‘yar shekara 9 ta hanyar fyade a cikin dakinsa ta hanyar tursasa ta da ƙarfin tsiya.

Lokacin da yake amsa tambayoyi, wanda ake zargin ya amsa laifin da ake zarginsa da aikata wa, har yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike, inda za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu don gurfanar da shi a gaban shari’a.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Next Post
bakin wake

Sabbin Hare-haren Kunar Bakin Wake A Borno Jama'a Na Fargabar Jiya Ta Dawo Yau

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.