• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Amsa Tambayoyi Game Da Ziyarar Da Sakatariyar Baitil-malin Amurka Ta Gudanar A Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Da yammacin yau Litinin ne jami’ai masu ruwa da tsaki daga ma’aikatar kudi ta kasar Sin, suka yi karin gaske ga manema labarai, game da ziyarar aiki da sakatariyar baitil-malin Amurka Janet Yellen ta gudanar a kasar Sin.

Jami’an sun ce Yellen ta gudanar da ziyarar aikinta tsakanin ranaikun 4 zuwa 9 ga watan nan na Afirilu, inda yayin ziyarar ta gana da firaministan kasar Sin Li Qiang, da mataimakin firaminista He Lifeng, da ma wasu karin jami’ai.

  • Hisba Ta Cafke Mata 7 Da Ake Zargi Da Satar Yadidduka A Kano
  • Roxy Danckwerts: Ina Matukar Son Rungumar Pandar Kasar Sin

Yayin tattaunawar jami’an, sassan Sin da na Amurka sun amince su hada karfi da karfe, wajen aiwatar da muhimman kudurori da shugabannin kasashen biyu suka cimma, da ci gaba da karfafa tattaunawa da hadin gwiwa a fannonin raya tattalin arziki da hada hadar kudade, kana su amince da aniyar samar da yanayi mai kyau na gudanar da cinikayya tsakanin kasashen biyu, da harkokin zuba jari tsakanin kamfanonin kasashen, da bunkasa alakar tattalin arziki mai tsafta, da daidaito tsakanin kasashen biyu.

Har ila yau, sassan biyu sun gamsu cewa, ko wace kasa tana da bukatar kare tsaron kan ta. To sai dai kuma Sin ta jaddada cewa, bai dace a dauki batun “Tsaron kasa” wani batu da ya game ko wane bangare ba. Sin ta bayyana damuwa game da yadda bangaren Amurka ke daukar matakai daban daban, irin su kakaba takunkuman dakile kamfanonin Sin, da dorawa Sin karin haraji, da wasu shingayen zuba jari, wanda hakan matakai ne na illata halastattun hakkoki, da moriyar kamfanoni da jama’ar kasar Sin, kana hakan bai dace da moriyar kamfanonin Amurka da jama’ar kasar ba.

A daya bangaren, Sin ta yi maraba da sanarwar da Amurka ta fitar, wadda ke cewa Amurka ba ta da niyyar raba-gari da Sin, kana Sin din na fatan Amurka za ta aiwatar da hakikanin matakai na dakatar da takunkumai, da shingayen da take sanyawa kamfanonin kasar Sin. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26
Daga Birnin Sin

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Next Post
Matakan Amurka Na Dakile Cinikayyar Ababen Hawa Masu Aiki Da Lantarki Na Sin Za Su Haifar Da Koma Bayan Cinikayya A Duniya

Matakan Amurka Na Dakile Cinikayyar Ababen Hawa Masu Aiki Da Lantarki Na Sin Za Su Haifar Da Koma Bayan Cinikayya A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.