• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bar Kasashe Masu Tasowa Da Jidalin Sauyin Yanayi

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
An Bar Kasashe Masu Tasowa Da Jidalin Sauyin Yanayi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Taron kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya kan sauyin yanayi karo na 29 ko COP29 a takaice, wanda aka kammala ranar Lahadi a birnin Baku na kasar Azarbaijan, ya haska irin babban rashin adalci dake tattare da ayyukan magance sauyin yanayi a duniya. Yayin da al’ummomi a kasashe masu tasowa ke ci gaba da fuskantar kalubale na magance matsalar sauyin yanayi, kokarinsu na ci gaba da fuskantar matsin lamba sakamakon rashin isassun tallafin kudi da tsari daga kasashe masu ci gaba. Wannan rashin daidaito ba wai kawai yana kawo cikas ga yaki na gama-gari da sauyin yanayi ba, har ma yana bayyana ma’auni biyu mai cike da damuwa game da yadda kasashe masu ci gaba ke cin gajiyar albarkatu yayin da kasashe masu tasowa ke fama da matsalolin da sarrafa wadannan albarkatu ke haifarwa.

 

Duk da kasancewar kasashe masu tasowa ke fitar da mafi karancin hayaki mai gurbata muhalli a tarihi, suna daukar matakai na ban mamaki game da kirkire-kirkire kan magance sauyin yanayi. Kasashe irin su Kenya, Brazil da Grenada sun yi fice a COP29 game da kyawawan ayyukansu da ke da nufin rage mummunar tasirin yanayi tare da habaka juriya. Sai dai nasarar wadannan yunkurin na bukatar makudan kudade. Alal misali, kasashen Afirka kadai za su bukaci kusan dala biliyan 280 a duk shekara nan da shekarar 2035 don daidaita matsalar sauyin yanayi da rage radadin da suke ciki, adadin da ya zarce karfinsu.

 

Taron ya cimma yarjejeniyar da kasashen da suka ci gaba za su rika ba da a kalla dalar Amurka biliyan 300 a duk shekara nan da shekara ta 2035, da nufin taimakawa kasashe masu tasowa wajen tunkarar tunbatsar teku da tasirin matsanancin sauyin yanayi. Wadannan kudaden za su je ga kasashe masu tasowa wadanda ke bukatar kudaden don sauyawa zuwa amfani da makamashi da ake iya sabuntawa, da daidaita dumamar yanayi da kuma daidaita barnar da tasirin sauyin yanayi ke haifarwa. Duk da cewa adadin ya ninka dala biliyan 100 a duk shekara na yarjejeniyar da za ta kare a shekara ta 2025, amma bai kai dalar Amurka tiriliyan 1.3 da kasashe masu tasowa ke bukata ba, kuma da yawa sun nuna takaici. (Mohammed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Dandalin Tattaunawar Liangzhu Karo Na Biyu A Birnin Hangzhou Na Lardin Zhejiang

Next Post

Netanyahu Ya Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Hezbollah

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

21 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

22 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

23 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

24 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

1 day ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

2 days ago
Next Post
Netanyahu Ya Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Hezbollah

Netanyahu Ya Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Hezbollah

LABARAI MASU NASABA

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

October 5, 2025
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.