• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bar Kasashe Masu Tasowa Da Jidalin Sauyin Yanayi

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
An Bar Kasashe Masu Tasowa Da Jidalin Sauyin Yanayi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Taron kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya kan sauyin yanayi karo na 29 ko COP29 a takaice, wanda aka kammala ranar Lahadi a birnin Baku na kasar Azarbaijan, ya haska irin babban rashin adalci dake tattare da ayyukan magance sauyin yanayi a duniya. Yayin da al’ummomi a kasashe masu tasowa ke ci gaba da fuskantar kalubale na magance matsalar sauyin yanayi, kokarinsu na ci gaba da fuskantar matsin lamba sakamakon rashin isassun tallafin kudi da tsari daga kasashe masu ci gaba. Wannan rashin daidaito ba wai kawai yana kawo cikas ga yaki na gama-gari da sauyin yanayi ba, har ma yana bayyana ma’auni biyu mai cike da damuwa game da yadda kasashe masu ci gaba ke cin gajiyar albarkatu yayin da kasashe masu tasowa ke fama da matsalolin da sarrafa wadannan albarkatu ke haifarwa.

 

Duk da kasancewar kasashe masu tasowa ke fitar da mafi karancin hayaki mai gurbata muhalli a tarihi, suna daukar matakai na ban mamaki game da kirkire-kirkire kan magance sauyin yanayi. Kasashe irin su Kenya, Brazil da Grenada sun yi fice a COP29 game da kyawawan ayyukansu da ke da nufin rage mummunar tasirin yanayi tare da habaka juriya. Sai dai nasarar wadannan yunkurin na bukatar makudan kudade. Alal misali, kasashen Afirka kadai za su bukaci kusan dala biliyan 280 a duk shekara nan da shekarar 2035 don daidaita matsalar sauyin yanayi da rage radadin da suke ciki, adadin da ya zarce karfinsu.

 

Taron ya cimma yarjejeniyar da kasashen da suka ci gaba za su rika ba da a kalla dalar Amurka biliyan 300 a duk shekara nan da shekara ta 2035, da nufin taimakawa kasashe masu tasowa wajen tunkarar tunbatsar teku da tasirin matsanancin sauyin yanayi. Wadannan kudaden za su je ga kasashe masu tasowa wadanda ke bukatar kudaden don sauyawa zuwa amfani da makamashi da ake iya sabuntawa, da daidaita dumamar yanayi da kuma daidaita barnar da tasirin sauyin yanayi ke haifarwa. Duk da cewa adadin ya ninka dala biliyan 100 a duk shekara na yarjejeniyar da za ta kare a shekara ta 2025, amma bai kai dalar Amurka tiriliyan 1.3 da kasashe masu tasowa ke bukata ba, kuma da yawa sun nuna takaici. (Mohammed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Dandalin Tattaunawar Liangzhu Karo Na Biyu A Birnin Hangzhou Na Lardin Zhejiang

Next Post

Netanyahu Ya Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Hezbollah

Related

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu
Daga Birnin Sin

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

2 minutes ago
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

2 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

2 hours ago
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

14 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

15 hours ago
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

16 hours ago
Next Post
Netanyahu Ya Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Hezbollah

Netanyahu Ya Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Hezbollah

LABARAI MASU NASABA

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.