ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bar Kasashe Masu Tasowa Da Jidalin Sauyin Yanayi

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Sauyin yanayi

Taron kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya kan sauyin yanayi karo na 29 ko COP29 a takaice, wanda aka kammala ranar Lahadi a birnin Baku na kasar Azarbaijan, ya haska irin babban rashin adalci dake tattare da ayyukan magance sauyin yanayi a duniya. Yayin da al’ummomi a kasashe masu tasowa ke ci gaba da fuskantar kalubale na magance matsalar sauyin yanayi, kokarinsu na ci gaba da fuskantar matsin lamba sakamakon rashin isassun tallafin kudi da tsari daga kasashe masu ci gaba. Wannan rashin daidaito ba wai kawai yana kawo cikas ga yaki na gama-gari da sauyin yanayi ba, har ma yana bayyana ma’auni biyu mai cike da damuwa game da yadda kasashe masu ci gaba ke cin gajiyar albarkatu yayin da kasashe masu tasowa ke fama da matsalolin da sarrafa wadannan albarkatu ke haifarwa.

 

Duk da kasancewar kasashe masu tasowa ke fitar da mafi karancin hayaki mai gurbata muhalli a tarihi, suna daukar matakai na ban mamaki game da kirkire-kirkire kan magance sauyin yanayi. Kasashe irin su Kenya, Brazil da Grenada sun yi fice a COP29 game da kyawawan ayyukansu da ke da nufin rage mummunar tasirin yanayi tare da habaka juriya. Sai dai nasarar wadannan yunkurin na bukatar makudan kudade. Alal misali, kasashen Afirka kadai za su bukaci kusan dala biliyan 280 a duk shekara nan da shekarar 2035 don daidaita matsalar sauyin yanayi da rage radadin da suke ciki, adadin da ya zarce karfinsu.

ADVERTISEMENT

 

Taron ya cimma yarjejeniyar da kasashen da suka ci gaba za su rika ba da a kalla dalar Amurka biliyan 300 a duk shekara nan da shekara ta 2035, da nufin taimakawa kasashe masu tasowa wajen tunkarar tunbatsar teku da tasirin matsanancin sauyin yanayi. Wadannan kudaden za su je ga kasashe masu tasowa wadanda ke bukatar kudaden don sauyawa zuwa amfani da makamashi da ake iya sabuntawa, da daidaita dumamar yanayi da kuma daidaita barnar da tasirin sauyin yanayi ke haifarwa. Duk da cewa adadin ya ninka dala biliyan 100 a duk shekara na yarjejeniyar da za ta kare a shekara ta 2025, amma bai kai dalar Amurka tiriliyan 1.3 da kasashe masu tasowa ke bukata ba, kuma da yawa sun nuna takaici. (Mohammed Yahaya)

LABARAI MASU NASABA

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95
Daga Birnin Sin

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
Next Post
Netanyahu Ya Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Hezbollah

Netanyahu Ya Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Hezbollah

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.