A yau Litinin ne aka bude taron koli na gina kasar Sin mai karfin al’adu na 2025 a birnin Shenzhen dake lardin Guangdong. Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin, kana darektan sashen kula da harkokin yada labarai na kwamitin kolin JKS Li Shulei, ya halarci taron tare da gabatar da muhimmin jawabi.
Baki da suka halarci taron sun yi imanin cewa, ya zama dole a dage wajen gudanar da manufar gina kasa mai karfin al’adu, da inganta yin kwaskwarima ga tsarin al’adu, da kara raya karfin kere-kere na al’adu, da kuma inganta cimma albarkatun al’adu.
Taken wannan taron shi ne “zurfafa yin gyare-gyare a tsarin al’adu, da kuma gudanar da ayyukan kirkire-kirkire da raya al’adu”, wanda sashen kula da harkokin yada labarai na kwamitin kolin JKS ya shirya. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp