• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Aikin Samar Da Wutar Lantarki Ta Mambila

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Labarai
0
An Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Aikin Samar Da Wutar Lantarki Ta Mambila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jihar Adamawa, ya bukaci gwamnatin tarayya da ta gaggauta fara aikin samar da wutar lantarkin ta madatsar ruwan (Mambila Hydro Power Project) a jihar Taraba, domin samun ci gaba a yankin baki daya.

Ahmadu Umaru Fintiri, ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a bukin cika shekaru 10, na Mai Martaba Sarkin Mambila, Dakta Shehu Baju II, a karamar hukumar Sardauna ta jihar Taraba.

  • Samar Da Tsaro: Ribadu Ya Yaba Wa Sarakunan Gargajiya A Adamawa
  • Za Mu Garzaya Kotun Koli Don Daukaka Kara Kan Zaben Gwamnan Adamawa- APC

Gwamnan wanda shi ne shugaban taron, da ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar Awwal Bamanga Tukur, ya jaddada mahimmancin irin wadannan ayyukan samar da wutar da cewa zai taimaka ga ababen more rayuwa da bunkasa tattalin arziki, da ma inganta rayuwar jama’a.

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, ya yi kira ga al’ummar yankin Mambila da su rungumi zaman lafiya da hadin kai, tare da sanin muhimmancin zaman lafiya wajen samar da ci gaba a tsakanin al’umma.

Gwamna Fintiri ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa da kokarin samar da ci gaba a tsakanin jihohin Adamawa da Taraba, ya kuma bayyana bukatar samar da ayyukan more rayuwa don bunkasa ci gaban yankin.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

A jawabinsa na fatan alheri a taron Sarkin Wukari, Aku Uka, wanda shi ne shugaban majalisar sarakunan gargajiyar jihar Taraba, Manu Ishaku, Ada Ali, ya bukaci mai masaukin biki da sarakunan gargajiya a jihar da su goyawa gwamnatin jihar baya wajen ganin an samar da zaman lafiya a jihar ya kuma yaba da goyon bayan da jama’ar masarautar ke baiwa masarautun gargajiya ta Mambila.

Da yake jawabin godiyar mai masaukin biki, Dakta Shehu Baju II, ya bayyana godiya da jin dadinsa ga duk wadanda suka bayar da gudumawa na ganin taron ya samu nasara, ya kuma yi godiya ta musamman ga hakimai da manyan baki, jama’a da masu hannu da shuni bisa goyon bayan da suka bayar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaMambilaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

2024: Gwamnan Kebbi Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Yi Wa Kasa Addu’a Da Marawa Tinubu Baya

Next Post

Shugaban CMG Ya Aike Da Sakon Barka Da Sabuwar Shekara Ga Al’ummun Ketare

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

5 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

5 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

15 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

17 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

18 hours ago
Next Post
CMG

Shugaban CMG Ya Aike Da Sakon Barka Da Sabuwar Shekara Ga Al’ummun Ketare

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.