• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Aikin Samar Da Wutar Lantarki Ta Mambila

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Mambila

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jihar Adamawa, ya bukaci gwamnatin tarayya da ta gaggauta fara aikin samar da wutar lantarkin ta madatsar ruwan (Mambila Hydro Power Project) a jihar Taraba, domin samun ci gaba a yankin baki daya.

Ahmadu Umaru Fintiri, ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a bukin cika shekaru 10, na Mai Martaba Sarkin Mambila, Dakta Shehu Baju II, a karamar hukumar Sardauna ta jihar Taraba.

  • Samar Da Tsaro: Ribadu Ya Yaba Wa Sarakunan Gargajiya A Adamawa
  • Za Mu Garzaya Kotun Koli Don Daukaka Kara Kan Zaben Gwamnan Adamawa- APC

Gwamnan wanda shi ne shugaban taron, da ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar Awwal Bamanga Tukur, ya jaddada mahimmancin irin wadannan ayyukan samar da wutar da cewa zai taimaka ga ababen more rayuwa da bunkasa tattalin arziki, da ma inganta rayuwar jama’a.

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, ya yi kira ga al’ummar yankin Mambila da su rungumi zaman lafiya da hadin kai, tare da sanin muhimmancin zaman lafiya wajen samar da ci gaba a tsakanin al’umma.

Gwamna Fintiri ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa da kokarin samar da ci gaba a tsakanin jihohin Adamawa da Taraba, ya kuma bayyana bukatar samar da ayyukan more rayuwa don bunkasa ci gaban yankin.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

A jawabinsa na fatan alheri a taron Sarkin Wukari, Aku Uka, wanda shi ne shugaban majalisar sarakunan gargajiyar jihar Taraba, Manu Ishaku, Ada Ali, ya bukaci mai masaukin biki da sarakunan gargajiya a jihar da su goyawa gwamnatin jihar baya wajen ganin an samar da zaman lafiya a jihar ya kuma yaba da goyon bayan da jama’ar masarautar ke baiwa masarautun gargajiya ta Mambila.

Da yake jawabin godiyar mai masaukin biki, Dakta Shehu Baju II, ya bayyana godiya da jin dadinsa ga duk wadanda suka bayar da gudumawa na ganin taron ya samu nasara, ya kuma yi godiya ta musamman ga hakimai da manyan baki, jama’a da masu hannu da shuni bisa goyon bayan da suka bayar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
CMG

Shugaban CMG Ya Aike Da Sakon Barka Da Sabuwar Shekara Ga Al’ummun Ketare

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.