• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Nuna Hotuna Da Shirye-Shiryen Bidiyo Da Matasan Kasa Da Kasa Suka Dauka Don Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafa MDD A Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
MDD

Jiya Talata 23 ga wata ne aka kaddamar da bikin nuna hotuna, da shirye-shiryen bidiyo da matasan sassan kasa da kasa suka dauka mai taken “One World: Shared Future”, wato “Duniya Daya: Makomar Bai Daya”, albarkacin murnar cika shekaru 80 da kafa Majalisar Dinkin Duniya a kasar Sin, wanda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, da hukumomin MDD dake nan kasar suka dauki nauyin shiryawa tare.

Mataimakin shugaban sashin fadakar da al’umma na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana shugaban CMG Shen Haixiong, ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo, a yayin taron da jami’an MDD, da jami’an diflomasiyyar kasa da kasa dake kasar Sin, da wakilan hukumomin majalisar dake nan kasar, da wakilan kafafen yada labaran kasa da kasa suka halarta.

A jawabin nasa, Mista Shen Haixiong ya ce, a shekaru 80 da suka wuce, MDD ta bayar da babbar gudummawa da ba za a iya mantawa ba, a fannonin wanzar da zaman lafiya, da samar da ci gaban duniya, gami da taimakawa cudanyar mabambantan wayewar kai. A nata bangare, kasar Sin tana sauke nauyin dake wuyanta a matsayin mambar dindindin a kwamitin sulhun MDD, tana mara wa majalisar baya wajen jagorantar batutuwan kasa da kasa, da kare ra’ayin cudanyar sassan kasa da kasa, tare da shaida wa dukkanin duniya yadda take sauke nauyi a matsayin babbar kasa.

A nata bangare kuwa, a matsayin muhimmiyar abokiyar hadin-gwiwa ta MDD, kafar CMG ta dade tana kula da harkokin majalisar, gami da gabatar da sakonta zuwa ga dukkanin duniya, da ruwaito rahotanni game da tsarin shugabancin duniya, da kafa gada da alaka tsakanin kasar Sin da dukkanin sassan kasa da kasa.

Ya ce a nan gaba kuma, CMG na fatan ci gaba da kokari tare da MDD, da kafafen yada labaran kasa da kasa gami da matasan duniya, don kawar da bambancin ra’ayi da sabani ta hanyar gabatar da hotuna ko shirye-shiryen bidiyo, ta yadda ra’ayin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya zai kara shiga cikin zukatan jama’a, da amsa shawarar tsarin shugabancin duniya. (Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki
Daga Birnin Sin

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

'Yansanda Sun Kama Mutane Biyu Da Laifin Garkuwa Da Wani Yaro Ɗan Shekara 10 A Neja

LABARAI MASU NASABA

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.