• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Ginin Sabuwar Hedikwatar Kungiyar ECOWAS

by CMG Hausa
3 years ago
ECOWAS

A jiya Lahadi ne aka aza tubalin ginin sabuwar hedikwatar kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yankin Afirka ta yamma ko ECOWAS, a birnin Abuja fadar mulkin Najeriya, aikin da kasar Sin za ta tallafa wajen gudanar da shi.

Ana sa ran ginin zai baiwa kungiyar damar tattare ayyukanta wuri guda, sabanin yadda a yanzu kungiyar ke da ofisoshi 3 a birnin Abuja.

  • Jihar Kebbi Zata Samu Tallafin Dala 350,000 – ECOWAS 

Shugabannin kasashen yammacin Afirka, ciki har da shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya, da takwarorinsa na Guinea Bissau da Saliyo, da kuma shugaban hukumar gudanarwar ECOWAS Omar Alieu Touray, da jakadan Sin a Najeriya Cui Jianchun, su ne suka jagoranci bikin aza tubalin ginin sabuwar hedikwatar.

Da yake tsokaci yayin kaddamar da aikin, jakada Cui Jianchun ya ce daukar nauyin ginin sabuwar hedikwatar ta ECOWAS da Sin ta yi, na nuni ga irin goyon bayan kasar ga ayyukan kungiyar, da ma kawancen gargajiyar dake tsakanin Sin da kasashen yammacin Afirka.

A nasa jawabin kuwa, shugaba Buhari ya bayyana aikin a matsayin shaidar goyon bayan Sin ga ECOWAS, kuma bayan kammalarsa, zai zamo matsugunin manyan ofisoshin ECOWAS 3, da suka hada da sakatariyar kungiyar, da kotun kasashe mambobin kungiyar, da kuma majalissar dokokin ECOWAS.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Buhari ya kara da cewa, aikin da kamfanin kasar Sin zai gudanar, zai zamo masaukin kasashen yankin yammacin Afirka baki daya, wanda zai wakilci hadin kai da ’yan uwantaka tsakanin kasashe mambobin kungiyar, zai kuma alamta karin aniyar mambobin kungiyar game da samar da ci gaba da dinkewar yankin.

Shi kuwa shugaban hukumar gudanarwar ECOWAS Omar Alieu Touray cewa ya yi, wannan rana ce mai muhimmancin gaske a tarihin kungiyar ECOWAS. Ya kuma jinjinawa gwamnatin kasar Sin bisa goyon bayanta ga kungiyar.

Alieu Touray ya kara da cewa, sabuwar hedikwatar za ta baiwa hukumar gudanarwar ECOWAS, damar karbar bakuncin daukacin jami’anta a wuri guda, ta yadda hakan zai inganta ayyukanta, da rage tsadar kudaden gudanarwa, da cimma karin nasarorin aiki. (Saminu Alhassan)

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Next Post
PDP Ta Nada Yakubu Dogara A Matsayin Mamba A Kwamitin Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa

PDP Ta Nada Yakubu Dogara A Matsayin Mamba A Kwamitin Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.