• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Ginin Sabuwar Hedikwatar Kungiyar ECOWAS

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Kaddamar Da Ginin Sabuwar Hedikwatar Kungiyar ECOWAS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Lahadi ne aka aza tubalin ginin sabuwar hedikwatar kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yankin Afirka ta yamma ko ECOWAS, a birnin Abuja fadar mulkin Najeriya, aikin da kasar Sin za ta tallafa wajen gudanar da shi.

Ana sa ran ginin zai baiwa kungiyar damar tattare ayyukanta wuri guda, sabanin yadda a yanzu kungiyar ke da ofisoshi 3 a birnin Abuja.

  • Jihar Kebbi Zata Samu Tallafin Dala 350,000 – ECOWAS 

Shugabannin kasashen yammacin Afirka, ciki har da shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya, da takwarorinsa na Guinea Bissau da Saliyo, da kuma shugaban hukumar gudanarwar ECOWAS Omar Alieu Touray, da jakadan Sin a Najeriya Cui Jianchun, su ne suka jagoranci bikin aza tubalin ginin sabuwar hedikwatar.

Da yake tsokaci yayin kaddamar da aikin, jakada Cui Jianchun ya ce daukar nauyin ginin sabuwar hedikwatar ta ECOWAS da Sin ta yi, na nuni ga irin goyon bayan kasar ga ayyukan kungiyar, da ma kawancen gargajiyar dake tsakanin Sin da kasashen yammacin Afirka.

A nasa jawabin kuwa, shugaba Buhari ya bayyana aikin a matsayin shaidar goyon bayan Sin ga ECOWAS, kuma bayan kammalarsa, zai zamo matsugunin manyan ofisoshin ECOWAS 3, da suka hada da sakatariyar kungiyar, da kotun kasashe mambobin kungiyar, da kuma majalissar dokokin ECOWAS.

Labarai Masu Nasaba

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

Buhari ya kara da cewa, aikin da kamfanin kasar Sin zai gudanar, zai zamo masaukin kasashen yankin yammacin Afirka baki daya, wanda zai wakilci hadin kai da ’yan uwantaka tsakanin kasashe mambobin kungiyar, zai kuma alamta karin aniyar mambobin kungiyar game da samar da ci gaba da dinkewar yankin.

Shi kuwa shugaban hukumar gudanarwar ECOWAS Omar Alieu Touray cewa ya yi, wannan rana ce mai muhimmancin gaske a tarihin kungiyar ECOWAS. Ya kuma jinjinawa gwamnatin kasar Sin bisa goyon bayanta ga kungiyar.

Alieu Touray ya kara da cewa, sabuwar hedikwatar za ta baiwa hukumar gudanarwar ECOWAS, damar karbar bakuncin daukacin jami’anta a wuri guda, ta yadda hakan zai inganta ayyukanta, da rage tsadar kudaden gudanarwa, da cimma karin nasarorin aiki. (Saminu Alhassan)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tura Mu Aka Yi Mu Sace Sanatan APC- Wasu ‘Yan Bindiga Da Suka Shiga Hannu

Next Post

PDP Ta Nada Yakubu Dogara A Matsayin Mamba A Kwamitin Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa

Related

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

7 hours ago
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

8 hours ago
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 
Daga Birnin Sin

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

9 hours ago
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

10 hours ago
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

11 hours ago
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

1 day ago
Next Post
PDP Ta Nada Yakubu Dogara A Matsayin Mamba A Kwamitin Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa

PDP Ta Nada Yakubu Dogara A Matsayin Mamba A Kwamitin Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.