Yau Talata, an kaddamar da shirin hadin gwiwar Sin da kasashen waje mai taken “Sabon Zamani da Sabon Fim” karo na biyu a birnin Changsha na lardin Hunan. Masana da masu nazari da kuma darektoci daga kasashen duniya sun halarci taron na wannan karo.
Hukumar harsunan waje ta kasar Sin da cibiyar shirye-shiryen labaran gaskiya da na talabijin da fina-finai na Babban Gidan Rediyo da Talabijin na kasar Sin wato CMG da wasu hukumomin sun tsara wannan shiri cikin hadin gwiwa, domin sa kaimi ga mutanen kasa da kasa da su gabatar da shirye-shiryen labaran gaskiya da gajerun bidiyoyin da suka dauka, inda za a ba da taimako gare su wajen kyautata da yada shirye-shiryensu. Kana, za su sami damar nuna shirye-shiryen da aka zaba ta manyan kafofin watsa labarai na kasar Sin da na kasashen duniya. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp