Jami’an rundunar hadin gwiwa ta JTF da suka kunshi jami’an tsaro daban-daban sun kama wasu mutane 26 da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a wani aikin tsaftace jihar daga masu aikata muggan laifi a yankin Sanata mai wakiltar Kogi ta Yamma.
Mai baiwa jihar shawara kan harkokin tsaro, Kwamanda Jerry Omodara (rtd) ne ya bayyana haka yayin da yake gabatar da wadanda ake zargin ga manema labarai a ranar Talata a Odo-Ape, karamar hukumar Kabba-Bunu ta jihar.
Omodara ya ce wannan farmakin da aka gudanar a cikin makonni biyu da suka gabata na daga cikin kokarin gwamnati na magance matsalar rashin tsaro a jihar.
A cewar Omodara, wadanda ake zargin sun hada da ‘yan asalin jihar da ake zargi da taimakawa ayyukan ‘yan bindiga ta hanyar samar musu da kayan aiki kamar abinci, ruwan sha, da sauransu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp