• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Sanda 3, Fararen Hula 3 A Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Sanata Ubah

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
An Kashe ‘Yan Sanda 3, Fararen Hula 3 A Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Sanata Ubah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mutane shida da suka kunshi har da ‘yansanda uku da fararen hula uku ne suka rasa rayukansu sakamakon harin da aka kai wa tawagar Sanatan da ke wakiltar mazabar Anambra ta Kudu, Sanata Ifeanyi Ubah.

Wasu ‘yan bindigan da ba a san ko su waye ba a ranar Lahadi sun farmaki tawagar Sanatan yankin Enugwu-Ukwu da ke karamar hukumar Njikoka a jihar Anambra.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in NSCDC Tare Da Garkuwa Da Mutum 3 A Ekiti

LEADERSHIP ta labarto cewa hamshakin mai hada-hadar Mai wanda shine mamallakin kamfanin Capital Oil and Gas, yana kan hanyarsa ta dawo daga cocin Anglican Synod a Ozubulu da ke karamar hukumar Ekwusigo zuwa wani otel din da ke zaune a Awka ne ‘yan bindigan dauke da muggan makamai farmaki tawagar a daidai Enugwu-Ukwu.

Kamar yadda ganau suka shaida, harin ya wakana ne da karfe 5 na yammacin ranar Lahadi. An ce Sanatan ya tsallake rijiya da baya ne sakamakon yana cikin mota wacce harsashi baya iya ratsata.

“Ba za mu iya ce ga kalar wadanda suka kawo harin nan zuwa yanzu ba. Kuma babu wanda ya san dalilin kai harin, amma kila ya kasance domin siyasa ko don harkarsa ta kasuwanci, za a iya tunanin komai,” a cewar majiyar.

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Kan wannan lamarin, cikin gaggawa gwamnan Jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo, ya yi Allahwadai da harin tare da tabbatar da cewa wadanda suka kai farmakin ba za su sha haka nan ba dole sai sun dandana kudarsu kuma sai doka ta yi aiki a kansu.

Ya ce, wannan harin zai sanya su kawo karshen ayyukan ta’addanci a jihar.

Sakataren yada labarai na Soludo, Mr Christian Aburime, ya nakalto cewa gwamnan ya mika ta’aziyyarsa ga Sanata Ubah da kwamishinan ‘yansandan jihar CP Echeng Echeng, bisa rashin jami’ai da suka yi sakamakon harin.

Kazalika, daya daga cikin manyan masu kalubalantar kujerar Sanatan a zaben 2023, Kuma Dan takarar Sanatar mazabar na jam’iyyar APGA, Hon. Chris Emeka Azubuogu, ya yi tir da harin da aka kai wa Ubah ya nuna kwarin guiwarsa na cewa gwamnan Jihar ba zai yi sako-sako da wannan lamarin ba har sai an hukunta masu hannu a lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Adadin Wadanda Suka Mutu Sakamakon Girgizar Kasa Mai Karfin Maki 6.8 Da Ta Afku A Lardin Sichuan Ya Kai 93

Next Post

Ministan Najeriya Ya Yi Maraba Da Kamfanonin Sin Da Su Zuba Jari A Kasar

Related

Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

52 minutes ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

3 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

3 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

4 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

6 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

9 hours ago
Next Post
Ministan Najeriya Ya Yi Maraba Da Kamfanonin Sin Da Su Zuba Jari A Kasar

Ministan Najeriya Ya Yi Maraba Da Kamfanonin Sin Da Su Zuba Jari A Kasar

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.