• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Sanda 3, Fararen Hula 3 A Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Sanata Ubah

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Sanata ubah

Mutane shida da suka kunshi har da ‘yansanda uku da fararen hula uku ne suka rasa rayukansu sakamakon harin da aka kai wa tawagar Sanatan da ke wakiltar mazabar Anambra ta Kudu, Sanata Ifeanyi Ubah.

Wasu ‘yan bindigan da ba a san ko su waye ba a ranar Lahadi sun farmaki tawagar Sanatan yankin Enugwu-Ukwu da ke karamar hukumar Njikoka a jihar Anambra.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in NSCDC Tare Da Garkuwa Da Mutum 3 A Ekiti

LEADERSHIP ta labarto cewa hamshakin mai hada-hadar Mai wanda shine mamallakin kamfanin Capital Oil and Gas, yana kan hanyarsa ta dawo daga cocin Anglican Synod a Ozubulu da ke karamar hukumar Ekwusigo zuwa wani otel din da ke zaune a Awka ne ‘yan bindigan dauke da muggan makamai farmaki tawagar a daidai Enugwu-Ukwu.

Kamar yadda ganau suka shaida, harin ya wakana ne da karfe 5 na yammacin ranar Lahadi. An ce Sanatan ya tsallake rijiya da baya ne sakamakon yana cikin mota wacce harsashi baya iya ratsata.

“Ba za mu iya ce ga kalar wadanda suka kawo harin nan zuwa yanzu ba. Kuma babu wanda ya san dalilin kai harin, amma kila ya kasance domin siyasa ko don harkarsa ta kasuwanci, za a iya tunanin komai,” a cewar majiyar.

LABARAI MASU NASABA

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Kan wannan lamarin, cikin gaggawa gwamnan Jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo, ya yi Allahwadai da harin tare da tabbatar da cewa wadanda suka kai farmakin ba za su sha haka nan ba dole sai sun dandana kudarsu kuma sai doka ta yi aiki a kansu.

Ya ce, wannan harin zai sanya su kawo karshen ayyukan ta’addanci a jihar.

Sakataren yada labarai na Soludo, Mr Christian Aburime, ya nakalto cewa gwamnan ya mika ta’aziyyarsa ga Sanata Ubah da kwamishinan ‘yansandan jihar CP Echeng Echeng, bisa rashin jami’ai da suka yi sakamakon harin.

Kazalika, daya daga cikin manyan masu kalubalantar kujerar Sanatan a zaben 2023, Kuma Dan takarar Sanatar mazabar na jam’iyyar APGA, Hon. Chris Emeka Azubuogu, ya yi tir da harin da aka kai wa Ubah ya nuna kwarin guiwarsa na cewa gwamnan Jihar ba zai yi sako-sako da wannan lamarin ba har sai an hukunta masu hannu a lamarin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nijeriya
Labarai

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Labarai

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Next Post
Ministan Najeriya Ya Yi Maraba Da Kamfanonin Sin Da Su Zuba Jari A Kasar

Ministan Najeriya Ya Yi Maraba Da Kamfanonin Sin Da Su Zuba Jari A Kasar

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Sanata ubah

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.