Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta bayar da rahoton cewa, an yi asarar rayuka biyar tare da lalata dukiyoyin da darajarsu ta kai miliyan ₦273.7 a wasu gobara da ta tashi a fadin jihar a watan Mayun 2025.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Saminu Yusif Abdullahi ya fitar a ranar Alhamis, hukumar ta bayyana cewa ta samu jimillar kiran gaggawa guda 71 a watan da ya gabata, wanda ya kunshi kiraye-kirayen kashe gobara 55, ceto 9, da kuma kiran karya 7.
- Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno
- Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina
Duk da wannan rashin nasara da aka samu, hukumar ta bayyana cewa ta yi nasarar ceto dukiyoyi da aka kiyasta darajarsu ta kai miliyan ₦446.6 tare da samun nasarar ceto mutane biyar.
Daraktan hukumar kashe gobara a jihar, Alhaji Sani Anas ya bukaci jama’a da su sanya ido sosai, musamman ganin yadda bukukuwan Sallar layya ke gabatowa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp