• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Sabuwar Damar Kyautata Hulda Tsakanin Sin Da Hungary

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
An Samu Sabuwar Damar Kyautata Hulda Tsakanin Sin Da Hungary
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Ziyarar da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ta kai kasarmu tana cike da ma’anar tarihi.” In ji Viktor Orban, firaministan kasar Hungary, yayin da yake hira da wakilin CMG a jiya Alhamis. Amma ko me ya sa ya ce tana da ma’anar tarihi? Saboda ziyarar shugaban ta haifar da dimbin sakamako.

Yayin wannan ziyarar da shugaba Xi Jinping ya kai kasar Hungary, shugabannin kasashen 2 sun gabatar da hadaddiyar sanarwa, inda suka sanar da daga matsayin huldar dake tsakanin kasashen 2, daga huldar abota da ta shafi manyan tsare-tsare a dukkan bangarori, zuwa wata mai alaka da sabon zamani, wadda za ta jure duk wani mawuyacin hali.

  • Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 5.7 A Watanni Hudu Na Farkon Bana
  • Sin: Haramta Fitar Da Kwakwalwar Kwamfuta Ga Huawei Da Amurka Ta Yi “Barazana Ce Ga Kasuwanci”

Manazartan al’amuran kasa da kasa na ganin cewa, wannan ci gaba ya nuna cewa, wasu harkoki na huldar dake tsakanin kasashen 2, da suka hada da amincewa da juna ta fuskar siyasa, da matsaya daya da suka cimma bisa manyan tsare-tsare, da hadin kansu a kokarin daidaita wasu al’amura, dukkansu za su cimma wani sabon matsayi. Kana huldar dake tsakanin kasashen 2 za ta iya jure duk wani kalubale, a duk wani yanayin al’amuran kasa da kasa. Ban da haka, kasashen 2 sun kulla yarjeniyoyin hadin gwiwa fiye da 10, wadanda suka aza harsashi ga yunkurin habaka hadin kan kasashen 2 a nan gaba.

Wani abun lura shi ne, Mista Orban ya musanta zargin da aka yi wa kasar Sin, cewa wai akwai “matsalar yawan samar da kayayyaki fiye da kima” a kasar, da “bukatar kawar da hadari” a kasar, da dai sauransu. A ganinsa, ci gaban kasar Sin dama ce ga tattalin arzikin kasashen Turai, maimakon kalubale mai hadari. Maganarsa ta nuna gaskiya da sanin ya kamata, da niyyar kasar Hungary ta zurfafa hadin gwiwa tare da kasar Sin.

Za mu iya hangar yadda kasashen Sin da Hungary za su hada gwiwarsu a kokarinsu na tabbatar da zamanantarwar kasa, da neman samun ci gaba da walwala tare, abun da zai taimaki yunkurin zurfafa hadin gwiwar da ke tsakanin kasar Sin da kasashen gabashin nahiyar Turai na tsakiya. (Bello Wang)

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJapanSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shekaru 14 Bayan Rasuwar Yar’Adua: Wasu Nasarori Da Ya Cimma A Rayuwarsa

Next Post

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Wasu Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Ba Za A Fitar Wa Kayayyaki Ba

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

13 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

14 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

16 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

17 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

24 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

1 day ago
Next Post

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Wasu Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Ba Za A Fitar Wa Kayayyaki Ba

LABARAI MASU NASABA

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.