ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shiga Alhini A Nijar Bayan Harin ‘Yan Bindiga Ya Hallaka Sojoji 20

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Nijar

Gwamnatin Nijar ta ayyana zaman makokin kwanaki uku bayan rasuwar sojojinta 20 da farar hula daya lokacin wani harin ta’addanci da ya rutsa da su a Kauyen Tassia na yankin Tilabery.

Lamarin ya faru ne a misalin karfe 10 na safiya a Kauyen Tassia Kudu da Band-jo dake karkarar Tera a Jihar Tilabery inda wasu ‘yan bindiga suka kai farmaki kan dakarun gwamnati, in ji sanarwar ma’aikatar tsaro wacce ta kara da cewa wasu sojoji tara sun jikkata sannan an lalata motoci biyu yayin da askarawan gwamnatin suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda da dama tare da lalata masu ab-aben hawa.

  • Lamarin Fanshon Tsofaffin Shugabanni A Nijeriya
  • Shugaban Bankin Duniya Ya Yi Tsokaci Kan Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin

Jama’ar kasa na nuna juyayi dangane da yadda matsalar tsaro ke haddasa asa-rar rayukan jami’an tsaro da farar hula duk da matakan da hukumomi ke cewa suna dauka.

ADVERTISEMENT

Gundumar Tera da ke matsayin yankin da Nijar ke iyaka da Burkina Faso na daga cikin wuraren da ‘yan ta’adda suka zafafa kai hare-hare a ‘yan watannin nan lamarin da ya tilasta wa mutane da dama neman mafaka .

Wani masani akan sha’anin tsaro Abass Moumouni na fassara lalacewar ya-nayin da karancin matakan hadin gwiwa saboda haka ya shawarci kasashen kawancen AES su gaggauta zartar da ayyukan rundunar da suka sanar cewa sun samar a watannin baya,

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

Jamhuriyar Nijar da ke kewaye da kasashen da ke fama da ayyukan kungiyoyi masu ikirarin jihadi na fuskantar hare-haren ta’addanci a yankunanta da dama musamman Jihar Tilabery dake iyaka da Burkina Faso da Mali.

Hakan ya sa sojojin kasar kifar da gwamnatin farar hula a watan Yulin 2023, haka kuma sabbin hukumomin sun kori sojojin kasashen Yammaci saboda zarginsu da rashin yin wani tabbas a yunkurin daidaita al’amura tare da maye gurabensu da dakarun Rasha masu aikin horo da nufin samo bakin zare, sai dai da alama har yanzu da sauran rina a kaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga
Kasashen Ketare

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Next Post
A Inter Miami Zan Yi Ritaya – Messi

A Inter Miami Zan Yi Ritaya – Messi

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.