• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shiga Alhini A Nijar Bayan Harin ‘Yan Bindiga Ya Hallaka Sojoji 20

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Nijar

Gwamnatin Nijar ta ayyana zaman makokin kwanaki uku bayan rasuwar sojojinta 20 da farar hula daya lokacin wani harin ta’addanci da ya rutsa da su a Kauyen Tassia na yankin Tilabery.

Lamarin ya faru ne a misalin karfe 10 na safiya a Kauyen Tassia Kudu da Band-jo dake karkarar Tera a Jihar Tilabery inda wasu ‘yan bindiga suka kai farmaki kan dakarun gwamnati, in ji sanarwar ma’aikatar tsaro wacce ta kara da cewa wasu sojoji tara sun jikkata sannan an lalata motoci biyu yayin da askarawan gwamnatin suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda da dama tare da lalata masu ab-aben hawa.

  • Lamarin Fanshon Tsofaffin Shugabanni A Nijeriya
  • Shugaban Bankin Duniya Ya Yi Tsokaci Kan Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin

Jama’ar kasa na nuna juyayi dangane da yadda matsalar tsaro ke haddasa asa-rar rayukan jami’an tsaro da farar hula duk da matakan da hukumomi ke cewa suna dauka.

Gundumar Tera da ke matsayin yankin da Nijar ke iyaka da Burkina Faso na daga cikin wuraren da ‘yan ta’adda suka zafafa kai hare-hare a ‘yan watannin nan lamarin da ya tilasta wa mutane da dama neman mafaka .

Wani masani akan sha’anin tsaro Abass Moumouni na fassara lalacewar ya-nayin da karancin matakan hadin gwiwa saboda haka ya shawarci kasashen kawancen AES su gaggauta zartar da ayyukan rundunar da suka sanar cewa sun samar a watannin baya,

LABARAI MASU NASABA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Jamhuriyar Nijar da ke kewaye da kasashen da ke fama da ayyukan kungiyoyi masu ikirarin jihadi na fuskantar hare-haren ta’addanci a yankunanta da dama musamman Jihar Tilabery dake iyaka da Burkina Faso da Mali.

Hakan ya sa sojojin kasar kifar da gwamnatin farar hula a watan Yulin 2023, haka kuma sabbin hukumomin sun kori sojojin kasashen Yammaci saboda zarginsu da rashin yin wani tabbas a yunkurin daidaita al’amura tare da maye gurabensu da dakarun Rasha masu aikin horo da nufin samo bakin zare, sai dai da alama har yanzu da sauran rina a kaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?
Kasashen Ketare

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

September 28, 2025
Next Post
A Inter Miami Zan Yi Ritaya – Messi

A Inter Miami Zan Yi Ritaya – Messi

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.