• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shiga Rudani Saboda Rashin Isar Tirelolin Shinkafar Tallafi Wasu Jihohi

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Labarai, Siyasa
0
An Shiga Rudani Saboda Rashin Isar Tirelolin Shinkafar Tallafi Wasu Jihohi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jihohi kadan ne suka karbi tirela 20 na tallafin shinkafar da gwamnatin tarayya ta ware wa kowacce jihohi da ke fadin kasar nan, inda zuwa lokacin rubuta wannan labari aka shiga rudani ganin yadda wasu jihohi da dama tirelolin shinkafar ba su iso gare su ba.

Wani bincike da aka gudanar a karshen makon da ya gabata ya nuna cewa babu wata jihar arewa da ta samu shinkafar sai dai Jihar Kano, yayin da a yankin jihohin kudu maso yamma suka amshi nasu illa Oyo ce kawai ta yi ikirarin cewa motocin ba sun iso.

  • Jihohi 11 Sun Kammala Jigilar Dawo Da Alhazansu 
  • 2027: Fafutukar Jan Akalar Jam’iyyar PDP Ta Koma Jihohi

A jihohin kudu maso kudu, da suka hada da Akwa-Ibom, Ribas da Bayelsa jami’an sun tabbatar da samun tallafin, yayin da wasu suka ce ba su isa ba.

Gwamnatin Jihar Delta ta ce har zuwa ranar Juma’a ba a samu shinkafar ba, yayin da jami’an jihohin Edo da Kuros Ribas ba su amsa nasu ba.

A ranar Litinin da ta gabata ne gwamnatin tarayya ta ce ta ware tireloli na shinkafa 740 ga jihohi 36 na tarayya da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Ana sa ran kowace jiha ciki har da Abuja za samu tiraloli guda 20 masu dauke da buhu shinkafa 1,200 na kilogiram 25 kowanne, sannan kuma za a raba shinkafar ga marasa galihu a cikin al’umma.

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai na fadar shugaban kasa a karshen taron majalisar zartarwa ta tarayya, wanda Shugaban kasa Bola Tinubu ya jagoranta a zauren majalisar da ke fadar shugaban kasa a Abuja.

Ministan wanda ke tare da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya ce shugaban kasar ya umarci ministan noma da ya tabbatar an samar da abinci ga ‘yan Nijeriya.

Ya kuma bayyana cewa an raba tirelolin shinkafar ne don ganin an daidaita kuncin rayuwa da ake fama da su a kasar, yana mai cewa ana sa ran gwamnonin jihohin za su raba motocin ga marasa galihu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: RiceShinkafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN

Next Post

Tsakanin Dangote Da Mahukuntan Fetur: Ina Muka Dosa?

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

2 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

2 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

3 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

3 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

5 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

6 hours ago
Next Post
Tsakanin Dangote Da Mahukuntan Fetur: Ina Muka Dosa?

Tsakanin Dangote Da Mahukuntan Fetur: Ina Muka Dosa?

LABARAI MASU NASABA

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.