• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Wallafa Bayanin Xi Jinping A Jaridar Saudiyya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Wallafa Bayanin Xi Jinping A Jaridar Saudiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa birnin Riyadh na kasar Saudiyya, don halartar taron koli na farko, na Sin da kasashen Larabawa, da taron koli na Sin da kasashen kungiyar hadin kan yankin Gulf ko GCC, tare da kai ziyartar aiki a kasar, an wallafa bayanin da Xi ya rubuta a jairdar Riyadh, mai taken “Yaukaka dankon zumunta, samar da makoma mai haske”.

Bayanin ya ce, tun bayan da aka kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu, alakar Sin da Saudiyya na bunkasa yadda ya kamata. Kasar Sin za ta yi amfani da wannan dama, don karfafa dangantakar abuta tare da Saudiyya bisa manyan tsare-tsare daga dukkan fannoni, da kara hadin-gwiwa don nuna adawa da shisshigin da sauran kasashe ke yi, da neman ci gaba cikin ‘yanci.

  • Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

Kana, kasashen biyu za su yi kokari tare, don hade shawarar “ziri daya da hanya daya” tare da “muradun samar da ci gaba na Saudiyya zuwa shekara ta 2030”. Bugu da kari, kasashen biyu, za su fadada mu’amala da juna a fannonin da suka shafi harkokin Majalisar Dinkin Duniya, da kasashen G20 da kungiyar hadin-kan Shanghai wato SCO da sauransu, a wani mataki na wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Gabas ta Tsakiya, da samar da ci gaba a duk fadin duniya baki daya.

Bayanin Xi ya kuma ce, Sin babbar kasa ce dake kokarin shimfida zaman lafiya da ci gaba a duniya, da kara samar da sabbin damammaki ga kasa da kasa, ciki har da na Larabawa, don yaukaka dankon zumunta, da samar da makoma mai haske tare da ‘yan uwa kasashen Larabawa.

Bugu da kari, kwanan baya shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ba da amsar sako ga wakilan masu sha’awar koyon Sinanci na kasar Saudiyya, inda ya karfafa zukatan matasan Saudiyya, domin su yi kokarin koyon Sinanci, ta yadda za su taimaka wajen zurfafa zumuncin dake tsakanin kasar Sin da kasar Saudiyya, da ma tsakanin kasar Sin da kasashen Larabawa.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

A cikin sakon nasa, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, koyon harsuna na sauran kasashe, zai ingiza zumuncin dake tsakanin al’ummomin kasashen, da taka rawa kan gina kyakkyawar makomar bil Adama ta bai daya.

A kwanakin da suka gabata ne, matasan Saudiyya masu sha’awar koyon Sinanci sama da 100, suka aike da wasiku ga shugaba Xi domin shaida masa sakamakon da suka samu yayin da suke koyon Sinanci, inda suka bayyana cewa, suna son kara fahimtar kasar Sin, tare kuma da zurfafa zumuncin dake tsakanin kasar Sin da kasar Saudiyya.

A halin da ake ciki yanzu, an riga an shigar da darasin Sinanci cikin manhajan ba da ilmi na Saudiyya, haka kuma an kafa sana’ar ilmi dake da nasaba da Sinanci a jami’ai 9 a kasar. (Mai fassarawa: Murtala Zhang, Jamila daga CMG Hausa)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci Emefiele Kan Takaita Cire Kudade 

Next Post

Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Dakatar Da Sabon Tsarin CBN Na Kayyade Cire Kudi

Related

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Daga Birnin Sin

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

48 minutes ago
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

2 hours ago
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

3 hours ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

4 hours ago
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

6 hours ago
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

24 hours ago
Next Post
Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Dakatar Da Sabon Tsarin CBN Na Kayyade Cire Kudi

Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Dakatar Da Sabon Tsarin CBN Na Kayyade Cire Kudi

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.