• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Wallafa Bayanin Xi Jinping A Jaridar Saudiyya

by CMG Hausa
3 years ago
Xi Jinping

Bayan da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa birnin Riyadh na kasar Saudiyya, don halartar taron koli na farko, na Sin da kasashen Larabawa, da taron koli na Sin da kasashen kungiyar hadin kan yankin Gulf ko GCC, tare da kai ziyartar aiki a kasar, an wallafa bayanin da Xi ya rubuta a jairdar Riyadh, mai taken “Yaukaka dankon zumunta, samar da makoma mai haske”.

Bayanin ya ce, tun bayan da aka kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu, alakar Sin da Saudiyya na bunkasa yadda ya kamata. Kasar Sin za ta yi amfani da wannan dama, don karfafa dangantakar abuta tare da Saudiyya bisa manyan tsare-tsare daga dukkan fannoni, da kara hadin-gwiwa don nuna adawa da shisshigin da sauran kasashe ke yi, da neman ci gaba cikin ‘yanci.

  • Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

Kana, kasashen biyu za su yi kokari tare, don hade shawarar “ziri daya da hanya daya” tare da “muradun samar da ci gaba na Saudiyya zuwa shekara ta 2030”. Bugu da kari, kasashen biyu, za su fadada mu’amala da juna a fannonin da suka shafi harkokin Majalisar Dinkin Duniya, da kasashen G20 da kungiyar hadin-kan Shanghai wato SCO da sauransu, a wani mataki na wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Gabas ta Tsakiya, da samar da ci gaba a duk fadin duniya baki daya.

Bayanin Xi ya kuma ce, Sin babbar kasa ce dake kokarin shimfida zaman lafiya da ci gaba a duniya, da kara samar da sabbin damammaki ga kasa da kasa, ciki har da na Larabawa, don yaukaka dankon zumunta, da samar da makoma mai haske tare da ‘yan uwa kasashen Larabawa.

Bugu da kari, kwanan baya shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ba da amsar sako ga wakilan masu sha’awar koyon Sinanci na kasar Saudiyya, inda ya karfafa zukatan matasan Saudiyya, domin su yi kokarin koyon Sinanci, ta yadda za su taimaka wajen zurfafa zumuncin dake tsakanin kasar Sin da kasar Saudiyya, da ma tsakanin kasar Sin da kasashen Larabawa.

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

A cikin sakon nasa, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, koyon harsuna na sauran kasashe, zai ingiza zumuncin dake tsakanin al’ummomin kasashen, da taka rawa kan gina kyakkyawar makomar bil Adama ta bai daya.

A kwanakin da suka gabata ne, matasan Saudiyya masu sha’awar koyon Sinanci sama da 100, suka aike da wasiku ga shugaba Xi domin shaida masa sakamakon da suka samu yayin da suke koyon Sinanci, inda suka bayyana cewa, suna son kara fahimtar kasar Sin, tare kuma da zurfafa zumuncin dake tsakanin kasar Sin da kasar Saudiyya.

A halin da ake ciki yanzu, an riga an shigar da darasin Sinanci cikin manhajan ba da ilmi na Saudiyya, haka kuma an kafa sana’ar ilmi dake da nasaba da Sinanci a jami’ai 9 a kasar. (Mai fassarawa: Murtala Zhang, Jamila daga CMG Hausa)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
Daga Birnin Sin

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
Next Post
Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Dakatar Da Sabon Tsarin CBN Na Kayyade Cire Kudi

Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Dakatar Da Sabon Tsarin CBN Na Kayyade Cire Kudi

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.