• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Wallafa Bayanin Xi Jinping A Jaridar Saudiyya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Wallafa Bayanin Xi Jinping A Jaridar Saudiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa birnin Riyadh na kasar Saudiyya, don halartar taron koli na farko, na Sin da kasashen Larabawa, da taron koli na Sin da kasashen kungiyar hadin kan yankin Gulf ko GCC, tare da kai ziyartar aiki a kasar, an wallafa bayanin da Xi ya rubuta a jairdar Riyadh, mai taken “Yaukaka dankon zumunta, samar da makoma mai haske”.

Bayanin ya ce, tun bayan da aka kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu, alakar Sin da Saudiyya na bunkasa yadda ya kamata. Kasar Sin za ta yi amfani da wannan dama, don karfafa dangantakar abuta tare da Saudiyya bisa manyan tsare-tsare daga dukkan fannoni, da kara hadin-gwiwa don nuna adawa da shisshigin da sauran kasashe ke yi, da neman ci gaba cikin ‘yanci.

  • Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

Kana, kasashen biyu za su yi kokari tare, don hade shawarar “ziri daya da hanya daya” tare da “muradun samar da ci gaba na Saudiyya zuwa shekara ta 2030”. Bugu da kari, kasashen biyu, za su fadada mu’amala da juna a fannonin da suka shafi harkokin Majalisar Dinkin Duniya, da kasashen G20 da kungiyar hadin-kan Shanghai wato SCO da sauransu, a wani mataki na wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Gabas ta Tsakiya, da samar da ci gaba a duk fadin duniya baki daya.

Bayanin Xi ya kuma ce, Sin babbar kasa ce dake kokarin shimfida zaman lafiya da ci gaba a duniya, da kara samar da sabbin damammaki ga kasa da kasa, ciki har da na Larabawa, don yaukaka dankon zumunta, da samar da makoma mai haske tare da ‘yan uwa kasashen Larabawa.

Bugu da kari, kwanan baya shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ba da amsar sako ga wakilan masu sha’awar koyon Sinanci na kasar Saudiyya, inda ya karfafa zukatan matasan Saudiyya, domin su yi kokarin koyon Sinanci, ta yadda za su taimaka wajen zurfafa zumuncin dake tsakanin kasar Sin da kasar Saudiyya, da ma tsakanin kasar Sin da kasashen Larabawa.

Labarai Masu Nasaba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

A cikin sakon nasa, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, koyon harsuna na sauran kasashe, zai ingiza zumuncin dake tsakanin al’ummomin kasashen, da taka rawa kan gina kyakkyawar makomar bil Adama ta bai daya.

A kwanakin da suka gabata ne, matasan Saudiyya masu sha’awar koyon Sinanci sama da 100, suka aike da wasiku ga shugaba Xi domin shaida masa sakamakon da suka samu yayin da suke koyon Sinanci, inda suka bayyana cewa, suna son kara fahimtar kasar Sin, tare kuma da zurfafa zumuncin dake tsakanin kasar Sin da kasar Saudiyya.

A halin da ake ciki yanzu, an riga an shigar da darasin Sinanci cikin manhajan ba da ilmi na Saudiyya, haka kuma an kafa sana’ar ilmi dake da nasaba da Sinanci a jami’ai 9 a kasar. (Mai fassarawa: Murtala Zhang, Jamila daga CMG Hausa)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci Emefiele Kan Takaita Cire Kudade 

Next Post

Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Dakatar Da Sabon Tsarin CBN Na Kayyade Cire Kudi

Related

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Daga Birnin Sin

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

5 hours ago
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

6 hours ago
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

7 hours ago
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

8 hours ago
“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale
Daga Birnin Sin

“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale

9 hours ago
Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing
Daga Birnin Sin

Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing

10 hours ago
Next Post
Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Dakatar Da Sabon Tsarin CBN Na Kayyade Cire Kudi

Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Dakatar Da Sabon Tsarin CBN Na Kayyade Cire Kudi

LABARAI MASU NASABA

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

September 10, 2025
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

September 10, 2025
Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

September 10, 2025
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

September 10, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

September 10, 2025
“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale

“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale

September 10, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

September 10, 2025
Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya

Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya

September 10, 2025
Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing

Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.