• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yaba Da Ra’ayin Kasar Sin Kan Zaman Lafiya Da Ci Gaba A Yankin Kahon Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Yaba Da Ra’ayin Kasar Sin Kan Zaman Lafiya Da Ci Gaba A Yankin Kahon Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon shugaban kasar Habasha, Mulatu Teshome ya bayyana cewa, an yaba da shawarar da kasar Sin ta gabatar, game da batun zaman lafiya da ci gaba a yankin kahon Afirka (HOA) a wani mataki na tallafawa kasashen yankin tinkarar kalubalen tsaro, da ci gaba da shugabanci, dake addabar su.

Daga ranar 20 zuwa 21 ga watan Yunin da ya gabata ne, aka gudanar da taron zaman lafiya da shugabanci na gari da raya kasa tsakanin Sin da yankin kahon Afirka karo na farko a birnin Addis Ababa, fadar mulkin kasar Habasha.

  • Sin Ta Yi Saurin Samun Karuwar Hukumomin Kula Da Hakkin Mallakar Fasaha

Babban taron zaman lafiya da ci gaban yankin, ya hallara ministoci da manyan jami’an gwamnatin kasashen yankin kahon Afirka, da suka hada da Habasha, da Kenya, da Sudan, da Sudan ta Kudu, da Somaliya, da Uganda da kuma Djibouti, da kuma Xue Bing, wakilin musamman na ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin mai kula da harkokin yankin kahon Afirka.

Tsohon shugaban kasar ta Habasha ya jaddada cewa, zaman lafiya da kwanciyar hankali na da muhimmanci ga ci gaban kowace kasa, inda ya ba da misali da kwarewar kasar Sin wajen samun bunkasuwa cikin lumana.

Ya bayyana cewa, labarin nasarorin da kasar Sin ta samu, da ci bunkasar tattalin arzikin kasar, sun samu ne sakamakon yadda kasar take zaune lafiya har ma da makwabtanta.

Labarai Masu Nasaba

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Don haka, ya ce muna bukatar al’umma mai zaman lafiya da kwanciyar hankali, kuma idan babu zaman lafiya da kwanciyar hankali, babu wanda zai zo ya zuba mana jari.”

Ya kara da cewa, kasashen yankin kahon Afirka sun gamsu cewa, muna bukatar zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, kuma kokarin da kasar Sin ke yi na saukakawa da kuma hada kan kasashen dake makwabtaka da juna, don tattauna batun zaman lafiya da tsaro da ci gaba na da matukar muhimmanci.

Ya ce, yana fatan kasar Sin za ta ci gaba da karfafa wa yankin gwiwa, wajen tattauna batun zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Kuma idan Habasha da makwabtanta suna zaman lafiya, hakika za mu ci gajiyar hakan.” (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Fita Daga Kungiyar Kamfe Ta Tinubu Kan Takarar Musulmi Da Musulmi – Sanata Abbo

Next Post

An Bayyana Dangantakar Sin Da Afrika A Matsayin Mai Gagarumar Tasiri

Related

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

20 minutes ago
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

18 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

19 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

21 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

22 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Next Post
An Bayyana Dangantakar Sin Da Afrika A Matsayin Mai Gagarumar Tasiri

An Bayyana Dangantakar Sin Da Afrika A Matsayin Mai Gagarumar Tasiri

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.