• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Bikin Kaddamar Da Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Mutane Masu Bukata Ta Musamman Ta Asiya A Hangzhou

by CGTN Hausa
2 years ago
Hangzhou

Yau Lahadi 22 ga wata ne, aka yi bikin kaddamar da gasar wasannin motsa jiki ta mutane masu bukata ta musamman ta kasashen Asiya karo na 4, a babban filin wasa na Olympics dake birnin Hangzhou na lardin Zhejiang dake gabashin kasar Sin. 

Kwamitin shirya gasar wasannin motsa jiki ta Olympics ta mutane masu bukata ta musamman ta kasashen Asiya, da kwamitin shirya gasar wasannin motsa jiki ta mutane masu bukata ta musamman ta Asiya ta Hangzhou, sun gudanar da taron manema labarai a yau Lahadi 22 ga wata da yamma, inda suka bayyana cewa, an riga na shirya tsaf domin gudanar da gasar wasannin motsa jiki ta mutane masu bukata ta musamman ta Asiya karo na 4 a birnin na Hangzhou.

  • Tinubu Ya Sadaukar Da Kai Ga Manufofin Nijeriya Da Afrika A Duniya – Minista
  • Abin Da Ya Sa Muka Sa Takin Zamani Cikin Tallafin Jama’a – Gwamnan Filato

Babban mai magana da yawun gasar ta bana, Chen Weiqiang ya bayyana cewa, gasar ta bana tana kunshe da manyan wasanni 22, hade da wasu kanana 564, wadda za ta samu halartar mutane kusan 5200 daga kasashe da yankuna 44, ciki har da ‘yan wasanni kusan 3100, da jami’an tawagogin kasa da kasa sama da 2090. Har ila yau, jami’an kula da fasahohi sama da 1550 da ‘yan jaridu fiye da 3090 su ma za su halarci gasar, abun da ya sa ta zama irinta mafi kasaita a tarihi.

Mista Chen ya kuma ce, an tanadi na’urori da kayayyaki na musamman da dama, a wani kokari na hidimtawa mahalarta masu bukata ta musamman, da samar musu da tabbaci don su halarci gasar yadda ya kamata.

Rahotannin sun kuma ruwaito cewa, tawagar kasar Sin na kunshe da mutane 723 a bana, ciki har da ‘yan wasanni 439, wadanda za su halarci dukkan manyan wasanni 22, da wasu kananan guda 397. (Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Next Post
Dabi’ar Saba Alkawarin Da Maza Ke Yi Ga Matan Da Za Su Aura

Dabi’ar Saba Alkawarin Da Maza Ke Yi Ga Matan Da Za Su Aura

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.