• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fargabar Wasu Leburori 3 Sun Mutu Sakamakon Ƙasa Ta Rufto Musu A Nasarawa

by Muhammad
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Al'ajabi, Manyan Labarai
0
Ana Fargabar Wasu Leburori 3 Sun Mutu Sakamakon Ƙasa Ta Rufto Musu A Nasarawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana fargabar wasu leburori uku da suke aikin hakar kasa a yammacin ranar Lahadin sun mutu bayan da wata kasa ta afko kansu a wani kauye da ake kira Unguwan Ayaba da ke karamar hukumar Keffi a jihar Nasarawa.

Ma’aikatan suna ta tono jar kasa tare da loda ta a cikin wata motar dakon kasa a wurin da suke hako kasar, sai kwatsam kasar ta yanko ta afka musu ta binne mutum hudu daga cikinsu.

  • Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa
  • Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Tabbatar Da Zaɓen Sule A Matsayin Gwamnan Nasarawa

An ce daya daga cikinsu an yi sa a ya tsallake rijiya da baya domin ya samu ya tsira daga karkashin kasar da ta danne su, sai dai ya samu raunuka yayin da sauran mutum ukun har yanzu ake kan tono ba a gansu ba.

Masu aikin ceto mutanen da mazauna kauyukan da suka hada da ‘yan uwan ​​wadanda abin ya shafa sun killace wurin domin tono gawarwakin ma’aikatan uku, sun fara aikin tonon tun da yammacin ranar Lahadi lokacin da abun ya faru, amma abin ya ci tura har zuwa lokacin kawo wannan rahoton.

Daya daga cikin masu aikin sa kai a wurin, Saliu Abdullahi, ya ce sun shafe fiye da sa’o’i biyu suna aikin tono ma’aikatan, ya kara da cewa ba za su bar wurin ba har sai sun hako gawarwakin ma’aikatan uku.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Shima mataimakin shugaban kungiyar masu Tipper da ke karamar hukumar Keffi, Aminu Sunusi, ya ce sun aika da injin tona domin a samu a gaggauta aikin ceto mutanen.

Sunusi ya kara da cewa za su dauki kwararan matakai don kaucewa irin matsalar da ake ciki da dakile afkuwar irin wannan hadari a nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KasaNasarawaRuftawaRuftowar kasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi: Sin Na Fatan Hade Dabarun Raya Kasa Da Jamaica

Next Post

AFCON 2023: Afirika Ta Kudu Ta Lallasa Ƙasar Namibiya Da Ci 4-0

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

15 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

19 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

20 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
AFCON 2023: Afirika Ta Kudu Ta Lallasa Ƙasar Namibiya Da Ci 4-0

AFCON 2023: Afirika Ta Kudu Ta Lallasa Ƙasar Namibiya Da Ci 4-0

LABARAI MASU NASABA

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.