• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Auren Bogi: An Garkame Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Zambar Fiye Da Naira Miliyan 9

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Auren Bogi: An Garkame Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Zambar Fiye Da Naira Miliyan 9
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kama wani dan Nijeriya mai suna Johnson a Birnin Delhi bisa laifin damfarar wata ‘yar kasar Indiya daga Rajnandgaon, Chhattisgarh da karyar zai aure ta.

‘Yansandan Rajnandgaon sun cafke Johnson, wanda ake zargi da damfarar matar da ke da lakhs din kudi bisa zargin yin aure.

  • Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Hada Karfi Da Karfe Wajen Samar Da Yanayin Da Zai Dace Da Warware Matsalar Sudan
  • EU Ta Ware Euro Miliyan 1 Don Tallafa Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Da Kwalara Suka Shafa A Nijeriya

‘Yansanda sun bayyana cewa Johnson yana zaune a Delhi a asirce, tun bayan karewar biza da fasfo dinsa.

A cewar ‘yansandan, wanda ake zargin ya kirkiro bayanan karya a shafin intanet auren inda kuma aka jera bayanan wanda aka kashe.

Da farko ya ja hankalin matar kuma ya tabbatar mata da cewa shi dan kasuwa ne da ke zaune a Birtaniya yana shirin fadada kasuwancinsa zuwa Indiya.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Ana zargin wanda ake tuhumar ya tuntubi matar ne ta hannun abokinsa, inda ya ce ya makale a filin jirgin saman Delhi kuma yana bukatar kudi don musayar kudin Burtaniya da yake da shi.

Rahul Deb Sharma, Sufeto na ‘yansanda a Rajnandgaon, ya ce, “Ya ci zarafin matar kuma ya yaudare ta Rufee 15,72,000 (kimanin Naira 9,100,000) tare da taimakon abokin aikinsa.”

Daga baya, lokacin da wacce aka damfara ta yi kokari ta kira shi, ta ji wayarsa a kashe.

Da ta fahimci cewa an yi mata zamba ne, matar ta kai kara hukumar ‘yansandan Dongargarh da laifin zamba.

“Mun fara bincike kan korafin mai bukata. Tare da taimakon wani rukunin intanet, an gano cewa wanda ake zargin yana zaune a Delhi. Kungiyarmu ta kai farmaki a gidansa na Delhi inda ta kama shi, “in ji Sharma.

“Wanda ake zargi Johnson mazaunin Nijeriya ne. Ya yaudari ‘yan mata da yawa ya zuwa yanzu. Muna kokarin samun karin bayani ta hanyar tambayoyi.”

‘Yansandan sun kuma lura cewa Johnson yana kusa da shekaru 40. Hukumomi sun kwato kwamfutar tafi-da-gidanka da wayoyin hannu hudu daga hannun wanda ake zargin, kuma an kulle asusun ajiyarsa na banki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Filato Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Tuhuma Da Laifin Safarar Kananan Yara

Next Post

Kudin Kirifto: An Cafke Dan Nijeriya Da Laifin Damfarar ‘Yan Australiya Dala Miliyan 8

Related

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

46 minutes ago
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

2 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

3 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

11 hours ago
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata
Labarai

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

11 hours ago
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

17 hours ago
Next Post
Kudin Kirifto: An Cafke Dan Nijeriya Da Laifin Damfarar ‘Yan Australiya Dala Miliyan 8

Kudin Kirifto: An Cafke Dan Nijeriya Da Laifin Damfarar ‘Yan Australiya Dala Miliyan 8

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

October 3, 2025
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

October 3, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.