• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Auren Gata : Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Aurar Da Mata 300

byUmar Faruk
2 years ago
Auren gata

Gwamnatin jihar Kebbi karkashin jagorancin Gwamna Nasir Idris tare da hadin gwiwar gidauniyar Nafisa Nasir Charity Development Foundation (NANAS) sun aurar da mata 300 a garin Birnin Kebbi tare da shawartar ma’auratan da su kasance masu sada zumunci da son juna.

Bikin wanda ya gudana a fadar Mai Martaba Sarkin Gwandu, Gidauniyar NANAS ce ta shirya wanda matar Gwamnan, Hajiya Nafisa Nasir Idris ta kafa.

  • ‘Saurayin Da Muka Yi Alkawarin Aure Ya Fara Kula ‘Yan Mata Da Yawa, A Ba Ni Shawara’
  • Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Zauren Taro a Borrong, Demsa

Kakakin majalisar dokokin jihar Rt. Hon. Muhammad Usman Ankwe, shine ya wakilci gwamna a wajen bikin daurin auren inda ya bayyana cewa, za’a gudanar da irin wannan daurin auren lokaci-lokaci domin taimakawa marasa galihu maza da mata.

Dakta Nasir Idris ya ce, gwamnatinsa ta bayar da jimillar Naira miliyan 21 a matsayin sadaki ga matan da aka daura wa aure 300 da suka fito daga kananan hukumomin jihar 21, inda kowace amarya za ta samu sadaki Naira 70,000.

Auren gata

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Ya kara da cewa, gwamnatinsa ta kuma samar da kayan daki da kayan abinci ga dukkan ma’auratan domin karfafa wa aurensu .

Haka kuma Gwamnan ya Kara da bayyana cewa an daura auren ne bayan tattaunawa da malaman addinin Musulunci bisa tsarin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi, wanda ya baiwa mabiyansa izinin yin mubayi’ar aure don amfanin al’umma da kuma haifar da zuriya masu albarka.

Daga karshe ya shawarci ma’aurata da su mutunta dokokin aure, yana mai cewa dole ne ango ya kare hakki da hakkokin matarsa, haka kuma matan su kasance masu aminci da goyon bayan mazajensu.

Auren gata

A nata jawabin, Uwargidan Gwamnan Jihar, Hajiya Nafisa Nasir Idris wadda ita ce ta kafa NANAS FOUNDATION, ta bayyana matukar jin dadinta ga mijin nata da ya ba ta tallafin kayan daki da kayan masarufi wanda ya sanya aka yi gagarumin bikin aure.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
CMG Ya Kaddamar Da Biki Kafin Liyafar Bikin Bazara A New York

CMG Ya Kaddamar Da Biki Kafin Liyafar Bikin Bazara A New York

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version