• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

by Sulaiman
3 weeks ago
Zamfara

Tun bayan da Gwamna Dauda Lawal ya karɓi ragamar mulkin jijar Zamfara a watan Mayun 2023, jihar ta fara fuskantar wani sabon salo na shugabanci wanda ya shafi kusan dukkan fannoni na rayuwa — daga tsaro zuwa tattalin arziki, daga ilimi zuwa lafiya, daga gyaran hanyoyi zuwa sake gina tsarin gwamnati da al’umma, sannan ga zamanannen tsarin harkar sufuri.

 

A cikin kusan shekaru biyu kacal, Gwamna Lawal ya kafa tarihin da yawancin mazauna jihar ke ganin ya bambanta da abin da suka saba gani a baya, musamman wajen aiwatar da manufofin da suka tabo rayuwar jama’a kai-tsaye.

 

Tsaro: Babban fagen da Gwamna Dauda Lawal ya fara tinkara da jajircewa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

 

Ba abin mamaki ba ne cewa tsaro shi ne babban ƙalubalen da jihar Zamfara ta daɗe tana fama da shi. Daga Maradun zuwa Shinkafi, daga Anka zuwa Zurmi, matsalar ‘yan bindiga ta yi ƙatutu na tsawon shekaru.

 

Da yake karɓar mulki, Gwamna Dauda Lawal ya sanar da cewa “ba za a iya gina tattalin arziki ba idan tsoro ya mamaye ƙasa.”

 

Tun daga farkon watannin mulkinsa, ya kafa Kwamitin Tsaro na Musamman, wanda ke haɗa jami’an soja, ‘yan sanda, NSCDC da ‘yan sa-kai. Gwamnatin ta samar da motocin sintiri sama da 500, da kayan aikin zamani ga jami’an tsaro.

 

Har ila yau, an kafa Command and Control Centre a Gusau domin sa ido kan al’amuran tsaro ta hanyar amfani da fasahar zamani. Wannan mataki ya rage hare-hare a wasu yankuna, inda al’umma ke sake komawa gonakinsu da kasuwancinsu cikin natsuwa.

 

Tattalin Arziki da Ci gaban Sana’o’i

A bangaren tattalin arziki, gwamnatin Dauda Lawal ta mayar da hankali kan farfaɗo da ƙananan sana’o’i da bunƙasa harkar kasuwanci.

 

Ta ƙaddamar da Zamfara Economic Empowerment Programme (ZEEP), wanda ke bai wa matasa da mata tallafin jari da horo kan sana’o’i kamar ɗinki, noma, kiwo, sana’ar waya da ƙera kayayyakin gida.

 

Haka kuma, gwamnatin ta buɗe Industrial Cluster a Gusau domin ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin masu ƙananan masana’antu, tare da samar da tallafi daga Bankin Noma da na Masana’antu.

 

A cewar kwamishinan tattalin arziki, “Gwamna Lawal na son ganin Zamfara ta daina dogaro da kuɗin rabon asusun tarayya, ta koma jiha mai samar da abin more rayuwa.”

 

Ilimi: Sabon salo na sake gina makarantun gwamnati

Fannin ilimi shi ne ginshiƙin ci gaban kowace al’umma. A ƙarƙashin wannan gwamnati, an mayar da hankali wajen gyaran makarantu sama da 200, tare da samar da kujeru, littattafai, kayan koyarwa da gyaran gine-gine.

 

Gwamnati ta kuma dawo da malamai dubu ɗaya (1,000) da aka bar su ba tare da albashi ba a baya, sannan aka ƙaddamar da shirin “Back to School” domin dawo da yara daga kan titi zuwa aji.

 

Haka kuma, gwamnatin ta sake gyara Zamfara State University Talata-Mafara, inda aka ƙara sabbin sassa na kimiyya da fasaha tare da inganta wuraren kwana da ɗakin karatu.

 

Lafiya: Asibitoci suna sake farfaɗowa

A bangaren lafiya, gwamnatin ta ƙaddamar da Free Maternal and Child Healthcare Programme, wanda ke bai wa mata da yara ƙarƙashin shekaru biyar kulawa kyauta a asibitoci.

 

An gyara asibitoci 14 a faɗin jihar, ciki har da babban asibitin Gusau, da aka sake gina dakin haihuwa da dakin tiyata da kayan aiki na zamani.

 

Gwamnati ta kuma samar da motocin ɗaukar marasa lafiya (ambulance) a kowace ƙaramar hukuma, tare da tura sabbin ma’aikatan jinya, likitoci da masu jinya zuwa yankunan karkara.

 

Ayyukan Gina Hanyoyi da Tsarin Gine-gine

Gwamnatin Dauda Lawal ta ƙaddamar da aikin gine-ginen manyan hanyoyi kamar Gusau–Damba–Mayana, Zurmi–Bukkuyum, da Kaura Namoda–Birnin Magaji.

 

Har ila yau, an gyara titunan cikin garin Gusau, inda aka saka fitilun zamani da tsarin ban ruwa don rage ƙura da datti.

 

A cewar Gwamna Lawal, “titi ba kawai hanyar mota ba ce, ita ce hanyar ci gaban al’umma.”

 

Gudanar da Gwamnati da Gaskiya

Wani abu da ya bambanta wannan gwamnati da waɗanda suka shuɗe shi ne gaskiya. A karon farko, Zamfara ta kafa tsarin Open Budget Portal, inda kowa zai iya ganin yadda kuɗin gwamnati ke tafiya.

 

Gwamnatin ta kuma kafa Anti-Corruption and Due Process Bureau, domin tabbatar da cewa kowace kwangila yana bin ƙa’idar gaskiya da nagarta.

 

Matsayin Jama’a da Hangen Nesa

Yawancin mazauna jihar sun bayyana cewa wannan gwamnatin “ta shigo da sabuwar rayuwa.” A cewar wani ɗan kasuwa a Gusau, “A baya, an manta da mu gaba ɗaya. Amma yanzu muna ganin canji a zahiri.”

 

Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa burinsa shi ne “Zamfara ta zama misalin tsabta, ci gaba da daidaito a Arewa.”

 

A tsarin da yake ginawa, ya ƙunshi Zamfara 2050 Vision Plan, shiri mai dogon lokaci da ke nufin canja jihar daga karkacewar tsaro da talauci zuwa jihar da ke iya dogaro da kanta.

 

Kammalawa

A ƙarshe, shekaru biyu bayan hawansa mulki, Dauda Lawal ya kafa tubalin sabon sahu a Zamfara – sahun da ya haɗa da tsaro, ilimi, lafiya, da tattalin arziki.

 

Ko da yake har yanzu akwai ɗan burbushin ƙalubale na tsaro da tattalin arziki, yawancin ‘yan Zamfara na ganin cewa wannan gwamnatin ta fara canji daga tushe, kuma abin da ke buƙata shi ne ci gaba da ɗorewar gaskiya, aiki tuƙuru da haɗin kai.

 

Zamfara tana fuskantar sabon zamani. Kuma idan aka kiyaye wannan tafiya, akwai yiwuwar a ce a cikin ɗan lokaci, Dauda Lawal ya kafa sabon tarihin shugabanci a Arewa.

 

Rahoto na musamman daga Mahdi Musa Muhammad

Ƙaramin Edita, Blueprint Manhaja

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Manyan Labarai

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci
Nazari

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

September 11, 2025
Mataimakin shugaban kasa
Nazari

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025
Next Post
Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.