• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (5)

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
9 months ago
Ilimi

…ci gaba daga makon jiya

Wuraren da jami’in ilimi zai iya yin aiki

Jami’in ilimi shi kwarare ne wanda shi ke da alhakin shiryawa, aiwatarwa,da kuma lura da lura da lalle ana yin lamurran kamar yadda manufofin da tsare- tsaren ilimin suka dace a tafiyar da su.Suna iya yin aiki ta dukkan kowane yanayi,ko wurare da suka hada da makarantu, hukumoin gwamnati da kuma kamfanoi masu zaman kan su.Hanyar samun aikin shi tana farawa ne da mallakar takradar shedar digiri a bangaren ilimi ko kimiyyar zamantakewa, ko kuma wani darasi da yake da alka da aikin da za ayi.Bayan kammala karatun digirin su na farko suna iya yin digiri na biyu duk a bangaren ilmin ko kuma wani sashe da yake na musamman, bayan sun kammala digirinsu na fako, suna iya yin na biyu ta bangaren ilimi ko kuma wani bangare na musamman kamar, shugabancin ilimi, bunkasa darussan ilimi,ko yadda tsarin yake. Duk da haka akwai bukatar jami’an ilimi. Jami’an ilimi akwai bukatar su mallaki takardar shedar koyarwa ko kuma lasin,wannan kuma ya danganta ne kan irin gudunmawar da suke badawa da kuma inda ya dace su tsaya.

Da Zarar sun kammala karatunsu suka mallaki dukkan matakan ilimin da suka kamata su samu, jami’an ilimi suna iya suna iya samun ko mallakar matakin da ake bukatar su kai kamar na kwararru kan abubuwan da za a koyar, ko jagoran tafiyar da tsari, ko kuma mai koyar da Malami.Wadannan a yadda aka sani sun hada da aiki da Malamai da jami’an mulki domin samar da tsare- tsaren ilimi da gabatar da su wadanda suka yi daidai da muradan/ manufofi hukumomin.Ya yin da su jami’an ilimi suke samun kwarewa da hakan za isa su zama sun gane aikin nas kamar yadda kowa yake so,da hakan suna iya samun karin girma zuwa wasu mukamai kamar darektan ilimi, ko kuma babban jami’in Koyarwa.

Wadannan ayyukan sun hada lura da yadda ake inganta da aiwatar tsare- tsare da manufofin ilimi da sassa da kuma hukumomi.Matsayin jami’an ilimi a mukamin su sune ke da alhakin kula da yadda ake tafiyar kasafiun kudi, hadin kai da abokan hulda yadda za su rika kokarin samun tsare- tsaren ilimi da kuma kudaden taimako ko daukar nauyi.Bugu da kari akwai ilimin da aka tsara yadda za a koyar da shi, jami’in ilimi da yake da kwarewa sun ,mallaki dabaru masu yawa da wasu karin abubuwan da ake bukata daga wurinsu.Wadannan sun hada da saniun makamar yadda za ayi hulda da mutane da kuma yawon yadda za a nakalci yadda lamurra suke, da kuma sha’awa da nuna son koda wane lokacin ana bukatar koyon wani sabon abu.

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Hakanan ma akwai su yi aiki duk irin halin da suka samu kansu, su san yadda lamurran ilimi za su tafi kamar yadda ya dace.Ko mai dai menene hanyoyin ko wuraren da jami’an ilimi za su iya yin aiki suna da yawa da kuma yadda za su samu ci gaba ta kowane hali suka tsinci kansu.Ko dai suna aiki a makarantar lardi ko hukumar da ke karkashin gwamnati,ko hukumar wadda ita babu ruwanta da riba, jami’an ilimi suna taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da duk wadanda suke son ilimi ana koya masu ta nagartattar hanyar da za ta kasance da hanyoyin karuwa.

 

Irin ayyukan da jami’in ilimi zai iya yi

Jami’inilimi kwararre ne wanda kuma har ila yau alhakin tafiyar harkokin,manufofin,da tsare- tsaren ilimi suka rataya a wuyansa, wannan ma har ya hada da yadda za a cimma nasarar yin hakan.Suna yin ayyuka a hukumomi daban- daban da suka hada da makarantu, kwalejoji, jami’oi, da kuma hukumomin gwamnati.Babban aikin su shi ne samar da kuma gabatar da tsare- tsare wadanda za su taimakawa ci gaban lamurran ilimi.Hakanan ma suna aiki kafada- kafada da Malamai, ‘yan makaranta, Iyaye, da sauran masu fada aji, domin tabbatar da cewar na tafiyar da lamurran ilimi kamar yadda ya dace, su kuma wadanda ake koyawa suna fahimtar abinda ake koya masu. Hakanan ma ayyukan da za su iya yi jami’an ilimi suna da yawa sun kuma sha bamban.Suna ma iya yin aiki a bangarorin kamar su yadda za a tsara ci gaban koyarwa, horar da Malami,yadda za a rika bibiyar tsarin ilimi, da kuma binciken ilimi.Jami’an ilimi suna iya kasancewa wadanda suka kware a fannoni ko bangarori daban daban kamar karatun/ilimin rayuwar farko ta yaro, bangaren yaki da jahilci, ilimi na musamman, da kuma ilimin koyon sana’oi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
ASUU
Ilimi

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Next Post
An Kammala Aikin Tsugunar Da Mutane A Gundumar Tingri Ta Sin Bayan Bala’in Girgizar Kasa

An Kammala Aikin Tsugunar Da Mutane A Gundumar Tingri Ta Sin Bayan Bala'in Girgizar Kasa

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.