• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Yabon Dan Kuturu…

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ba A Yabon Dan Kuturu…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan mako ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya fadawa shugaban masu rinjaye na majalisar dattawan kasar Amurka Chuck Schumer, wanda ya jagoranci wata tawagar ’yan majalisar dokokin Amurka don kawo ziyara kasar Sin cewa, a wannan duniya mai cike da sauye-sauye da rudani, yadda kasashen Sin da Amurka za su daidaita, shi ne zai iya tabbatar da makomar bil Adama.

Shugaba Xi ya ce, a matsayinsu na manyan kasashe biyu, ya kamata Sin da Amurka su nuna himma, da hangen nesa, da kaiwa ga matsayin da kasashen duniya ke fata, da kokarin inganta jin dadin jama’arsu, da ingiza ci gaban bil Adama.

  • Sakamako Da Aka Samu Bayan Gina Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya
  • Daliban Cibiyar Koyar Da Ilmin Sana’a Ta Luban Dake Djibouti

Bugu da kari, yayin da duniya da ma zamani ke sauyawa, har yanzu tunanin tarihi na zaman lafiya tsakanin kasashen Sin da Amurka bai sauya ba, haka kuma babban burin jama’arsu na yin mu’amala da yin hadin gwiwa bai canja ba, kana fatan da kasashen duniya ke yi na samun kwanciyar hankali da bunkasuwar dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka bai sauya ba.

Ya kuma bukaci bangarorin biyu da su mutunta juna, su zauna tare cikin lumana, da yin hadin gwiwa domin samun nasara tare. Manufar kasashen 2 dai ita ce, su daidaita da kuma kyautata alakarsu, da samar da hanyar da ta dace don yin cudanya da juna a sabon zamani na tarihi.

A nasa bangare Schumer ya gabatar da ra’ayoyin da suka dace na bangaren Amurka, ya kuma bayyana aniyar karfafa tuntuba da tattaunawa da kasar Sin bisa gaskiya da mutunta juna, da kuma lura da bambance-bambance dake tsakaninsu bil hakki da gaskiya da kaucewa tayar da rikice-rikice, kuma Amurka ba za ta raba gari da Sin ba.

Labarai Masu Nasaba

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Haka ma yayin ziyarar da sakatariyar baitul malin Amurka Janet Yellen ta kawo kasar Sin ta bayyana aniyarta ta kara yaukaka alaka, da cudanya da hadin gwiwa, da mutunta juna tsakanin kasashen biyu. Amma da komarwa Amurka sai aka ji ta tana furta wasu manufofin Amurka da ba su dace ba kan kasar Sin., ta hanyar fakewa da batun tsaron kasa.

Wannan dai ba shi ne karon farko da ake jin kasashen biyu na furta irin wadannan kalamai ba, amma daga karshe sai a wayi gari Amurka ta sa kafa ta yi fatali da abin da ta furta ko aka cimma, matakin dake sake mayar da hannun agogon baya a hadin gwiwar kasashen dake zama mafiya karfin tattalin arziki a duniya.

Idan ba a manta ba, ko shi ma sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken yayin da ya kawo makamanciyar wannan ziyara kasar Sin a wannan shekara, ya furta irin wadannan kalamai na karfafa alaka da mutunta alkawuran da aka cimma, amma bayan komawarsa gida, sai aka ji shi yana furta wasu kalamai marasa dacewa game da alakar sassan biyu.

Masu fashin baki dai na cewa, ya dace Amurka ta rika nuna sanin ya kamata ta kuma cika alkawuran da ta yi, tare da daina neman bata sunan kasar Sin ko kakaba mata takunkuman da ko kadan ba su dace ba. Don haka, a wannan karon ma, ba za a yi saurin gaskata kalaman jagoran tawagar ’yan majalisun dokokin na Amurka ba. Masu iya magana na cewa, ba a yabon dan kuturu, sai ya shekara da dan yatsa.

Duniya dai ta zuba ido tare da fatan gwamnatin Amurka, za ta dauki hakikanin matakai domin ciyar da huldarta da Sin gaba yadda ya kamata, wadda ke da muhimmanci ba ma ga kasashen biyu ba, har ma ga duniya baki daya. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Cafke Mutum 3 Bisa Zargin Fashi Da Makami A Jihar Kano

Next Post

Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta

Related

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

12 hours ago
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
Daga Birnin Sin

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

13 hours ago
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

14 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

16 hours ago
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya
Daga Birnin Sin

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

17 hours ago
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

19 hours ago
Next Post
Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta

Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta

LABARAI MASU NASABA

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.