• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Amince Da Yi Wa Masu Daukar Nauyin Ta’addanci Shari’a A Sirrance Ba

by Ra'ayinmu
4 months ago
in Labarai
0
Ba Mu Amince Da Yi Wa Masu Daukar Nauyin Ta’addanci Shari’a A Sirrance Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Za a iya alakanta kokarin da Gwamnatin Tarayya mai ci ke kan yi, wajen gasar bunaka tattalin azriki da kuma inganta rayuwar ‘yan Nijeriya duba da cewa sun kasance, suna ci gaba da fuskantar matsin tattalin arziki da kuma ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro.

A yayin bude taron yaki da safararar haramtattun kudade da dakile biyan kudaden daukar nauyin ta’addanci tare da kuma yakar bazuwar kanannan makamai a hannun jama’a da aka gudanar a Abuja na 2025, Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya shedawa mahalarta taron cewa, Gwamnatinsa daidai da dabaraun dakile yakar ta’addanci, ta kasa wato NCTFS, ta karfafa karfinta tare da kuma ci gaba da zakulo masu daukar nauyin ta’addanci a kasar.

  • Sojoji Sun Tarwatsa Sansanin Lakurawa A Sokoto Da Kebbi, Tare Da Ƙwato Makamai
  • Babu Sauran Burbushin ‘Yan Ta’addan Lakurawa A Arewa Maso Yamma – Ministan Tsaro

Tinubu, ya  sanar da hakan ne, ta bakin Sakataren Gwamnatin Tarayya  Sanata George Akume, inda ya sanar da cewa, ta hanyar kokarin da ofishin Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara ta Musamman a Fannin Tsaro da kuma kokarin Akanta Janar kuma Ministan Shari’a ke yi, Gwamnatin Tarayya, a cikin shekaru biyu, ta samu nasarar gurfanarwa a gaban Kotu da kuma yankewa irin wadannan mutanen da ke daukar nauyin ta’adanci sama da 100 hukunci.

Mu a wannan Jaridar, muna jinjinawa Gwamnatin Tarayya, kan wannna nasarar, tare da kuma ba ta shawarar cewa, da ta kara kaimi, wajen yaki da duk wani na’ui na aikata manyan laifuka, musamman ayyukan ta’addanci, fashin Daji, garkuwa da mutane, tayar da kayar baya da kuma tayar da tashin tashina, a daukacin  fadin Nijeriya, musamman duba da cewa, wa’adannan ayyukan,  sun kai ga durkusar da kasar da kuma ‘yan kasar, biyo bayan vullar ta’addaci da kuma bayyanar masu hakilon a raba Nijeriya gida biyu.

Sai dai, wani hanzari ba gudu ba, bama goyon bayan yiwa masu daukar nauyin aikata ayyukan ta’addanci da kuma ‘yan ta’addar, Shari’a a, asirce.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

Hujjar mu a nan ita ce, kundin tsarin mulkin Nijeriya, sama yake da kowanne dan kasar da kuma sauran dokokin kasar, duba da cewa, kundin ya bayar da damar a yi Shari’ar a bisa adalci kuma a bayyane, ga wadanda ake tuhumar da aikata laifi.

Bugu da kari, dole ne mu tuhumi matakan da mahukuntan kasar suka dauka na yiwa wadanda ake tuhumar Shari’ar a, asirce.

Akwai dimbin tambayoyi a zukatan ‘yan Nijeriya wanda kuma suke bukatar amsa, misali, a ina ne aka cafke su? ta yaya ne, aka kama su? yaushe ne, aka gurfanar da su, a gaban Kotu? Shin an barsu sun dauki Lauyoyin da za su tsaya masu gaban Kotu? har tsawon wanne lokaci ne, suke ci gaba da fuskantar Shari’a kuma kan wanne laifi ne, Kotu ke tuhumarsu?, me ya sanya ake yi masu Sharia’a a, asirce?

Tabbas, ‘yan Nijeriya na bukatar amsar wadannan tambayoyin, duba da cewa, kamata ya yi, a ce, ana yin masu Shari’ar bisa bin ka’ida, ko dai mutum dan kasa ne ko kuma bakin haure ne, ya kamata a ce, ana yi masu Shari’ar a bayya ne.

Yi wa mutanen, Shari’ar a, asirce ya savawa ka’ida duba da cewa, kundin tsarin mulkin Nijeriya, ya tanadi a bai wa, duk wanda ake zargi, ‘yancin da yi masa adalaci, kan tuhumar da ake yi masa.

Wannan Shari’ar da ake yiwa mutanen a asirce, hakan ya jefa ‘yan Nijeriya a cikin  bakin duhun, sanin  hakikanin yadda Shari’ar ke tafiya, hujojin da aka gabatar a kansu a gaban Kotu tare da kuma cewar, wadanda Kotun ke tuhuma, a kan wanne takamaiman laifi ne, aka gurnar da su kuma wanne irin hukuncin da aka yanke masu.

Hakan ya nuna cewa, rashin bin ka’ida a yi masu Shari’ar, tare da taka dokar kasa da kuma take ‘yancin ‘yan Adam.

Kazalika, hakan ya sanya nuna rashin aminta da Gwamnatin Tarayya, na cewa, ko za yi hukuncin bisa gaskiya.

Abin tambaya a nan shi ne, ta yaya irin wadannan gungun tantiran ‘yan ta’addar, musamman ‘yan ta’addar Boko Haram da suka fara aikita ta’addancin su tun a 2009, a kuma ce wai za yi masu Shari’a asirce?

‘Yan Nijeriya na bukatar sanin shi wadanne mutane ne, ke taimakawa ‘yan ta’addar wajen aikata ta’asarsu.

A gafe daya kuma, ‘yan ta’addar na ci gaba da kai farmaki ga sansanonin dakarun soji tare da kuma hallaka su da kuma kashe sauran fararne Hula, ciki har da dattijai, mata da kuma yara, inda ta’asar ta su, ta mayar da yaran marayu, matan kuma suka zama zawarawa ba tare da sun aikatawa ‘yan ta’addar wani laifi ba.

‘Yan ta’addar, sun zama tamkar, wasu mala’ikun mutuwa sanadiyyar kisan da suke yi, hakan ya janyo tarwatsa mafarkin wadanda lamarin ya rutsa da su da kuma tarwatsa su, daga matsugunan su, da suka gada tun daga kaka da kakanni.

Har zuwa yau, ‘yan makarantar Boko, musamman ‘ya’ya mata ana ci gaba da yin garkuwa da su, a wasu sassan kasar nan, tare da kuma yadda ‘yan ta’addar ke tilasta su, su aure su da kuma sanya su a aikin bauta.

‘Yan Nijeriya na ci gaba da hadiye fishinsu duba da cewa, wadanda suka dauki nau’yin ‘yan ta’addar da suka aikata masu ta’asar, amma Gwamnatin Tarayya ta yi uwa ta kuma yi makarviya, wajen kin yiwa ‘yan ta’addar da masu daukar nauyinsu Shari’a a asirce.

A namu ra’ayin domin ‘yan Nijeriya su yi ammana da Shari’ar da ake yiwa wadnda ake tuhumar a, asirce, ya zama wajbi Gwamnatin Tarayaya ta bayyana su, ta hanyar wallafa sunayensu, hotunansu, kanannan hukumomin da suka fito da kuma jihohin su na haihuwa, irin laifin da suka aikata aka kaisu gidan kaso da kuma irin hukuncin da aka yanke masu, a cikin a Jaridun kasar.

Yin hakan zai bai wa kamfanoni masu zaman kansu yanke duk  wata nau’in hada-hadar kasuwanci da su da kuma hana hukumomin gwamnati daukar su, aiki.

Muna shawartar Gwamnatin Tarayya cewa, da ta sake yin tunani, kan dabarun da ta dauka, na yiwa wadnada ake tuhumar, Shari’ar asirce.

Daukar wannan shawarar na da matukar mahimmanci, musamman domin a tabbatar da yin gaskiya da adalci tare da kuma kare kimar ‘yancin Adam da kuma girmama  dokar kasa.

Hakazalika, Gwamnatin Tarayya, ta tabbatar da yi masu Sharia’r bisa gaskiya, a bar su, su dauki Lauyoyi da za su tsaya masu, kuma hujjojin da aka gabatar kan zarginsu, su kasance na gaskiya ne, wadanda kuma za a iya gabatarwa, a gaban Kotu.

Abu ne, mai kyau a yaki da ta’addanci, amma ya kamata a yi hakan, ta hanyar mutunta ‘yancin daidaikun mutane, tabbatar da yin gaskiya da adalci da kuma mutunta, ‘yancin ‘yan Adam.

Batun yi wa masu aikata ta’addanci Shari’a ko kuma masu daukar nauyin aikata ta’addanci a kasar nan a, asirce, abu ne da ya savawa turbar mulkin Dimokiradayyar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Shari'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Binciken CGTN: Tasaruffi A Cikin Sanyi Ya Daukaka Sunan Harbin Da Nuna Yakini Ga Habakar Tattalin Arzikin Sin

Next Post

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja…

Related

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta
Manyan Labarai

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

44 minutes ago
2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu
Labarai

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

4 hours ago
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa
Labarai

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

14 hours ago
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
Labarai

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

17 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

19 hours ago
bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

21 hours ago
Next Post
Zargin Yaudara: Wani Tela Ya Kashe Tsohuwar Masoyiyarsa A Kaduna

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja...

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

June 2, 2025
2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

June 2, 2025
Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.