• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Buƙatar Amincewar Sanusi Kan Tsare-tsarenmu Na Tattalin Arziki – Minista

by Sulaiman
9 months ago
Ministan Labarai

Gwamnatin Tarayya ta mayar da martani kan kalaman Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, kan tsare-tsaren gyaran tattalin arziki da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu take aiwatarwa, tana mai bayyana su a matsayin marasa amfani kuma na son rai.

A wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya fitar a ranar Laraba, ya bayyana cewa Nijeriya tana cikin wani muhimmin mataki da ke buƙatar matakan da suka dace da kuma ƙarfin hali domin magance manyan matsalolin tattalin arziki.

  • Bukatar Sanin Hakikanin Halin Da Tattalin Arzikin Nijeriya Ke Ciki
  • Jarumin Bollywood Saif Ali Khan Ya Tsallake Rijiya Da Baya

Ministan ya nuna jin daɗin sa kan yadda Sanusi ya amince da wasu tsare-tsaren gwamnati, amma ya nuna damuwa kan yadda Sarkin ya bayyana cewa ba zai goyi bayan gwamnati ba saboda wasu dalilai na son rai.

Ya ce: “Abin takaici ne yadda shugaba daga masarauta mai daraja da son tsare gaskiya da adalci zai fito fili ya ce ba zai faɗi gaskiya ba saboda dalilan kan sa.”

Ya jaddada cewa gyare-gyaren da gwamnatin ta yi, kamar daidaita farashin dala da kuma cire tallafin man fetur, sun zama dole domin magance shekaru na gazawa wajen gudanar da tattalin arzikin ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Idris ya bayyana cewa an fara ganin sakamakon waɗannan matakai ƙarara, wanda ya haɗa da ƙaruwar ajiyar kuɗaɗen waje, ƙaruwar ƙwarin gwiwar masu zuba hannun jari, da rage yawan bashin da ake biya.

Ministan ya bayyana cewa sukar da sarkin ya yi ba ta dace ba, musamman ganin cewa ya taɓa goyon bayan irin waɗannan matakan a baya. Ya yi kira ga Sanusi da ya fifita cigaban ƙasa a kan son rai.

Ya ce: “Gyaran Nijeriya tana buƙatar haɗin kai, mayar da hankali, da sadaukarwa daga dukkan masu ruwa da tsaki.
“Ya kamata shugabanni su zama jagororin cimma muradun cigaban ƙasa, ba masu tauye amanar jama’a ba.”

Idris ya sake tabbatar da aniyar gwamnatin ta bunƙasa tattalin arziki mai ɗorewa, tare da yin kira ga ’yan Nijeriya su ba da haɗin kai domin samun nasarar waɗannan tsare-tsare.

Ministan ya jaddada cewa gwamnati a shirye take don tattaunawa mai amfani da dukkan masu ruwa da tsaki, tare da tabbatar da cewa tana kan hanyar cika burin samar da ƙasa mai inganci ga kowa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole
Labarai

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU
Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara
Manyan Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
Next Post
Rikicin Masarautar Kano Ya Sake Daukar Sabon Salo

Rikicin Masarautar Kano Ya Sake Daukar Sabon Salo

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.