• English
  • Business News
Monday, July 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Buƙatar Amincewar Sanusi Kan Tsare-tsarenmu Na Tattalin Arziki – Minista

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Ministan Labarai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta mayar da martani kan kalaman Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, kan tsare-tsaren gyaran tattalin arziki da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu take aiwatarwa, tana mai bayyana su a matsayin marasa amfani kuma na son rai.

A wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya fitar a ranar Laraba, ya bayyana cewa Nijeriya tana cikin wani muhimmin mataki da ke buƙatar matakan da suka dace da kuma ƙarfin hali domin magance manyan matsalolin tattalin arziki.

  • Bukatar Sanin Hakikanin Halin Da Tattalin Arzikin Nijeriya Ke Ciki
  • Jarumin Bollywood Saif Ali Khan Ya Tsallake Rijiya Da Baya

Ministan ya nuna jin daɗin sa kan yadda Sanusi ya amince da wasu tsare-tsaren gwamnati, amma ya nuna damuwa kan yadda Sarkin ya bayyana cewa ba zai goyi bayan gwamnati ba saboda wasu dalilai na son rai.

Ya ce: “Abin takaici ne yadda shugaba daga masarauta mai daraja da son tsare gaskiya da adalci zai fito fili ya ce ba zai faɗi gaskiya ba saboda dalilan kan sa.”

Ya jaddada cewa gyare-gyaren da gwamnatin ta yi, kamar daidaita farashin dala da kuma cire tallafin man fetur, sun zama dole domin magance shekaru na gazawa wajen gudanar da tattalin arzikin ƙasa.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

An Sanya Wa Titin Shendam Sunan Marigayi Muhammadu Buhari

Idris ya bayyana cewa an fara ganin sakamakon waɗannan matakai ƙarara, wanda ya haɗa da ƙaruwar ajiyar kuɗaɗen waje, ƙaruwar ƙwarin gwiwar masu zuba hannun jari, da rage yawan bashin da ake biya.

Ministan ya bayyana cewa sukar da sarkin ya yi ba ta dace ba, musamman ganin cewa ya taɓa goyon bayan irin waɗannan matakan a baya. Ya yi kira ga Sanusi da ya fifita cigaban ƙasa a kan son rai.

Ya ce: “Gyaran Nijeriya tana buƙatar haɗin kai, mayar da hankali, da sadaukarwa daga dukkan masu ruwa da tsaki.
“Ya kamata shugabanni su zama jagororin cimma muradun cigaban ƙasa, ba masu tauye amanar jama’a ba.”

Idris ya sake tabbatar da aniyar gwamnatin ta bunƙasa tattalin arziki mai ɗorewa, tare da yin kira ga ’yan Nijeriya su ba da haɗin kai domin samun nasarar waɗannan tsare-tsare.

Ministan ya jaddada cewa gwamnati a shirye take don tattaunawa mai amfani da dukkan masu ruwa da tsaki, tare da tabbatar da cewa tana kan hanyar cika burin samar da ƙasa mai inganci ga kowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Sanin Hakikanin Halin Da Tattalin Arzikin Nijeriya Ke Ciki

Next Post

Rikicin Masarautar Kano Ya Sake Daukar Sabon Salo

Related

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

13 minutes ago
An Sanya Wa Titin Shendam Sunan Marigayi Muhammadu Buhari
Labarai

An Sanya Wa Titin Shendam Sunan Marigayi Muhammadu Buhari

6 hours ago
Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja
Manyan Labarai

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

8 hours ago
Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

9 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4

10 hours ago
Yadda Gwamnan Katsina Ya Tsira Daga Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Yadda Gwamnan Katsina Ya Tsira Daga Hatsarin Mota

11 hours ago
Next Post
Rikicin Masarautar Kano Ya Sake Daukar Sabon Salo

Rikicin Masarautar Kano Ya Sake Daukar Sabon Salo

LABARAI MASU NASABA

Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin

Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin

July 21, 2025
Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

July 21, 2025
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Hada Sassan Kasa Da Kasa

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Hada Sassan Kasa Da Kasa

July 21, 2025
Adadin Masu Amfani Da Intanet A Sin Ya Kai Sama Da Mutane Biliyan 1.12

Adadin Masu Amfani Da Intanet A Sin Ya Kai Sama Da Mutane Biliyan 1.12

July 21, 2025
Sin Ta Gina Tsarin Layin Dogo Da Manyan Hanyoyin Mota Da Na Aikewa Da Kunshin Sakwanni Mafi Girma A Duniya

Sin Ta Gina Tsarin Layin Dogo Da Manyan Hanyoyin Mota Da Na Aikewa Da Kunshin Sakwanni Mafi Girma A Duniya

July 21, 2025
Sin Ta Yi Tsayin Daka Kan Daidaita Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Siyasa Da Diflomasiyya

Sin Ta Yi Tsayin Daka Kan Daidaita Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Siyasa Da Diflomasiyya

July 21, 2025
Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna

Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna

July 21, 2025
An Sanya Wa Titin Shendam Sunan Marigayi Muhammadu Buhari

An Sanya Wa Titin Shendam Sunan Marigayi Muhammadu Buhari

July 21, 2025
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

July 21, 2025
Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

July 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.