• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Da Alaƙa Da Duk Wata Talla Ta Zambatar Al’umma – Rundunar Soji 

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Labarai
0
Ba Mu Da Alaƙa Da Duk Wata Talla Ta Zambatar Al’umma – Rundunar Soji 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar sojin Nijeriya ta 23 da ke Yola, ta gargadi jama’a game da wata sanarwar talla da ke yawo a kafofin sada-zumunta, kan wani taron bayar da agaji mai taken ‘A 3 Day Charity Exercise/10km Trek 2024’.

Rundunar ta ce, sanarwar ta yi ikirarin gudanar da bukin cika shekaru 25, na hidimar jin kai na kungiyar matan sojojin Nijeriya (NAOWA), da akace za’a gudanar da taron a ofishin jami’an soji da ke Yola daga ranar 8 zuwa 11 ga Fabrairu, 2024.

  • Rundunar Soji Ta Kudancin Sin Ta Gudanar Da Ayyukan Sintiri Na Dakarun Sojin Ruwa Da Na Sama A Tekun Kudancin Kasar
  • ‘Yansanda Sun Kama Dan Bindiga, Sun Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 8 A Taraba

Cikin sanarwar da mukaddashin jami’in hulda da jama’a na rundunar sojin da ke Yola, Laftanar Princewill Odoemenam, ya aikewa manema labarai, ta ci gaba da cewa “tallar ana zargin wani mutum mai suna AB Gofai AFOBREF da ya sanya wa hannu, ya ce shi ne Kwamanda, tare da bayar da lambar waya (08123497002).

“Tallar ta bukaci jama’a da su biya kudin talla ta Firstmonie Wallet da Palmpay asusun mai lamba 8132843616, a karkashinsa ansa sunan asusu Captain Jacub BD” inji sanarwar.

Rundunar ta ce “ba tare da wata shakka ba, ba mu da alaka da wannan sanarwa, bamu san wani Kwamanda mai suna AB Gofai ba, kuma bamu da duk wata alaka da wani mutum da aka ce Captain Jacub BD a cikin Runduna ta 23.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

“Muna gargadin jama’a sosai game da biyan duk wani kudi ga asusun da aka ambata, bugu da kari, rundunar soji ta 23, ta jaddada cewa babu irin wannan shirin gudanar da biki kamar yadda aka bayyana a sama.

“Mun nisanta kan mu da wannan tallar na bogi, tare da shawartar jama’a da su yi taka-tsan-tsan da kaurace wa duk wata kiraye-kiraye na talla, ko daukar nauyin gudanar da wani taron karya da aka ambata a sama.

“Rundunar Sojin Nijeriya, ta dauki al’amuran zamba da mazambata da muhimmanci, tana karfafa wa jama’a gwiwa da su kai rahoton duk wani abin da suke zargi ga hukumomin da suka dace” inji Princewill.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan bindigar SokotoRundunar sojojin NijeriyaYan yahoo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalar Tsaron Nijeriya: Ku Faɗi Alkairi Ko Ku Yi Shiru!

Next Post

AFCON 2023: Hasashe Ya Nuna Nijeriya Ce Za Ta Lashe Gasar Cin Kofin Afirika Ta Bana

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

2 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

4 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

6 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

7 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

8 hours ago
Next Post
AFCON 2023: Hasashe Ya Nuna Nijeriya Ce Za Ta Lashe Gasar Cin Kofin Afirika Ta Bana

AFCON 2023: Hasashe Ya Nuna Nijeriya Ce Za Ta Lashe Gasar Cin Kofin Afirika Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.