• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Da Alaƙa Da Duk Wata Talla Ta Zambatar Al’umma – Rundunar Soji 

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Soji

Rundunar sojin Nijeriya ta 23 da ke Yola, ta gargadi jama’a game da wata sanarwar talla da ke yawo a kafofin sada-zumunta, kan wani taron bayar da agaji mai taken ‘A 3 Day Charity Exercise/10km Trek 2024’.

Rundunar ta ce, sanarwar ta yi ikirarin gudanar da bukin cika shekaru 25, na hidimar jin kai na kungiyar matan sojojin Nijeriya (NAOWA), da akace za’a gudanar da taron a ofishin jami’an soji da ke Yola daga ranar 8 zuwa 11 ga Fabrairu, 2024.

  • Rundunar Soji Ta Kudancin Sin Ta Gudanar Da Ayyukan Sintiri Na Dakarun Sojin Ruwa Da Na Sama A Tekun Kudancin Kasar
  • ‘Yansanda Sun Kama Dan Bindiga, Sun Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 8 A Taraba

Cikin sanarwar da mukaddashin jami’in hulda da jama’a na rundunar sojin da ke Yola, Laftanar Princewill Odoemenam, ya aikewa manema labarai, ta ci gaba da cewa “tallar ana zargin wani mutum mai suna AB Gofai AFOBREF da ya sanya wa hannu, ya ce shi ne Kwamanda, tare da bayar da lambar waya (08123497002).

“Tallar ta bukaci jama’a da su biya kudin talla ta Firstmonie Wallet da Palmpay asusun mai lamba 8132843616, a karkashinsa ansa sunan asusu Captain Jacub BD” inji sanarwar.

Rundunar ta ce “ba tare da wata shakka ba, ba mu da alaka da wannan sanarwa, bamu san wani Kwamanda mai suna AB Gofai ba, kuma bamu da duk wata alaka da wani mutum da aka ce Captain Jacub BD a cikin Runduna ta 23.

LABARAI MASU NASABA

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

“Muna gargadin jama’a sosai game da biyan duk wani kudi ga asusun da aka ambata, bugu da kari, rundunar soji ta 23, ta jaddada cewa babu irin wannan shirin gudanar da biki kamar yadda aka bayyana a sama.

“Mun nisanta kan mu da wannan tallar na bogi, tare da shawartar jama’a da su yi taka-tsan-tsan da kaurace wa duk wata kiraye-kiraye na talla, ko daukar nauyin gudanar da wani taron karya da aka ambata a sama.

“Rundunar Sojin Nijeriya, ta dauki al’amuran zamba da mazambata da muhimmanci, tana karfafa wa jama’a gwiwa da su kai rahoton duk wani abin da suke zargi ga hukumomin da suka dace” inji Princewill.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Manyan Labarai

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa
Manyan Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba
Manyan Labarai

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Next Post
AFCON 2023: Hasashe Ya Nuna Nijeriya Ce Za Ta Lashe Gasar Cin Kofin Afirika Ta Bana

AFCON 2023: Hasashe Ya Nuna Nijeriya Ce Za Ta Lashe Gasar Cin Kofin Afirika Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.