• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Tauye Wa Kowa Damar Mallakar Katin Zabe A Kasar Nan Ba – INEC

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Ba Mu Tauye Wa Kowa Damar Mallakar Katin Zabe A Kasar Nan Ba – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta ƙaryata zargin ta hana mutum milyan 7 kammala rajistar mallakar katin zaɓe.

Sati ɗaya kafin jam’iyyun da su ka takarar zaɓen shugaban ƙasa su fara yaƙin nan zaɓen 2023, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce ba gaskiya ba ce zargin da ake yi ta tauye wa ‘yan Najeriya milyan 7 damar ƙasara rajistar da su ka fara ta manhajar INEC, domin mallakar katin rajistar zaɓe ba.

  • 2023: Mun Cire Sunayen Mutanen Da Suka Yi Rajistar Katin Zabe Sau Biyu —INEC

Cikin wata sanarwar da Kakakin Yaɗa Labaran INEC Festus Okoye ya fitar, ya bayyana cewa hukumar ta bayar da isasshen lokacin da duk wanda ya fara yin rajistar mallakar katin zaɓe a manhajar INEC, to ya je cibiyar yin rajista ido-da-ido ya kammala rajistar sa.

Okoye ya ce duk waɗanda ba su kammala ba, ko dai sun fara ne su ka watsar, ko kuma sun fara, daga baya kuma ba su kammala ba, sai su ka koma a cibiyoyin rajista ido-da-ido domin su yi a can ɗungurugum.

“An jawo hankalin INEC dangane da wasu rahotannin da ake yaɗawa cewa ana zargin INEC da tauye wa mutum milyan bakwai damar kallama rajistar su ido-da-ido, wadda su ka fara a shafin manhajar INEC ta intanet.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

“To ya kamata a sani cewa a gaskiya INEC ba ta tauye wa kowa damar kammala rajistar mallakar katin zaɓe ba. Don haka rahotannin ba gaskiya ba ce, ƙarairayi ne kawai.

“Tun a ranar 24 ga Yuni, 2021 INEC ta ƙirƙiri tsarin fara yin rajistar mallakar katin zaɓe ta manhajar hukumar. Ta yi haka domin rage wa jama’a jeƙala-jeƙala da ɓata lokaci a wurin yin rajista ido-da-ido.

“A bisa wannan tsari, idan mutum ya fara rajista a manhaja, to daga baya zai samu lokaci ya je cibiyar yin rajista ido-da-ido, inda za a ɗauki hoton sa da tambarin yatsun hannun sa, domin kammala rajista, inda daga nan sai ya jira mallakar katin shaidar yin zaɓe (PVC).” Inji Okoye, wanda Kwamishina ne na Ƙasa, kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da kan Jama’a na INEC.

“Mutum 10,487,977 su ka shiga manhajar INEC domin fara yin rajista, amma a cikin su, yayin da 3,444,378 ne kaɗai su kammala yin rajistar a cibiyoyin rajista ido-da-ido.

“Daga cikin 7,043,594 waɗanda ba su kammala yin ta su rajistar a cibiyoyin rajista ido-da-ido ba, mutum 4,161,775 sun yi ƙoƙarin fara yin rajista ta cikin manhaja, amma sai su ka watsar, su ka koma cibiyoyin rajista ido-da-ido su ka yi kai-tsaye.

“Wasu 2,881,819 kuma sun kammala fara rajista a manhaja, amma ba su kai kan su cibiyoyin rajista ido-da-ido sun kammala ba.” Cewar Okoye.

Idan ba a manta ba, kwanan baya ne dai ƙungiyar SERAP ta jagoranci wakilcin mutum 24 waɗanda su ka shigar da INEC ƙara a Babbar Kotun Tarayya, Abuja, su na neman kotu ta tilasta wa INEC cewa ta ba su dama, su da sauran ‘yan Najeriya milyan 7 su kammala yin rajistar su da su ka fara.

A ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/1662/2022, sun shaida wa kotu cewa ba su samu damar kammala rajistar su ba har wa’adin da INEC ta gindiya za a rufe yin rajista ya cika.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shirin Tallafa Wa Manoma Mata ‘Yan Kasuwa Na GEEP Ya Kankama A Bauchi

Next Post

2023: Mace 1 Ce Ta Fito Takarar Shugaban Kasa Da Wasu 380 A Kujerun Majalisar Tarayya – INEC

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

47 minutes ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

3 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

15 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

20 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

22 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

23 hours ago
Next Post
2023: Mace 1 Ce Ta Fito Takarar Shugaban Kasa Da Wasu 380 A Kujerun Majalisar Tarayya – INEC

2023: Mace 1 Ce Ta Fito Takarar Shugaban Kasa Da Wasu 380 A Kujerun Majalisar Tarayya - INEC

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.