• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Tauye Wa Kowa Damar Mallakar Katin Zabe A Kasar Nan Ba – INEC

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Ba Mu Tauye Wa Kowa Damar Mallakar Katin Zabe A Kasar Nan Ba – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta ƙaryata zargin ta hana mutum milyan 7 kammala rajistar mallakar katin zaɓe.

Sati ɗaya kafin jam’iyyun da su ka takarar zaɓen shugaban ƙasa su fara yaƙin nan zaɓen 2023, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce ba gaskiya ba ce zargin da ake yi ta tauye wa ‘yan Najeriya milyan 7 damar ƙasara rajistar da su ka fara ta manhajar INEC, domin mallakar katin rajistar zaɓe ba.

  • 2023: Mun Cire Sunayen Mutanen Da Suka Yi Rajistar Katin Zabe Sau Biyu —INEC

Cikin wata sanarwar da Kakakin Yaɗa Labaran INEC Festus Okoye ya fitar, ya bayyana cewa hukumar ta bayar da isasshen lokacin da duk wanda ya fara yin rajistar mallakar katin zaɓe a manhajar INEC, to ya je cibiyar yin rajista ido-da-ido ya kammala rajistar sa.

Okoye ya ce duk waɗanda ba su kammala ba, ko dai sun fara ne su ka watsar, ko kuma sun fara, daga baya kuma ba su kammala ba, sai su ka koma a cibiyoyin rajista ido-da-ido domin su yi a can ɗungurugum.

“An jawo hankalin INEC dangane da wasu rahotannin da ake yaɗawa cewa ana zargin INEC da tauye wa mutum milyan bakwai damar kallama rajistar su ido-da-ido, wadda su ka fara a shafin manhajar INEC ta intanet.

Labarai Masu Nasaba

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

“To ya kamata a sani cewa a gaskiya INEC ba ta tauye wa kowa damar kammala rajistar mallakar katin zaɓe ba. Don haka rahotannin ba gaskiya ba ce, ƙarairayi ne kawai.

“Tun a ranar 24 ga Yuni, 2021 INEC ta ƙirƙiri tsarin fara yin rajistar mallakar katin zaɓe ta manhajar hukumar. Ta yi haka domin rage wa jama’a jeƙala-jeƙala da ɓata lokaci a wurin yin rajista ido-da-ido.

“A bisa wannan tsari, idan mutum ya fara rajista a manhaja, to daga baya zai samu lokaci ya je cibiyar yin rajista ido-da-ido, inda za a ɗauki hoton sa da tambarin yatsun hannun sa, domin kammala rajista, inda daga nan sai ya jira mallakar katin shaidar yin zaɓe (PVC).” Inji Okoye, wanda Kwamishina ne na Ƙasa, kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da kan Jama’a na INEC.

“Mutum 10,487,977 su ka shiga manhajar INEC domin fara yin rajista, amma a cikin su, yayin da 3,444,378 ne kaɗai su kammala yin rajistar a cibiyoyin rajista ido-da-ido.

“Daga cikin 7,043,594 waɗanda ba su kammala yin ta su rajistar a cibiyoyin rajista ido-da-ido ba, mutum 4,161,775 sun yi ƙoƙarin fara yin rajista ta cikin manhaja, amma sai su ka watsar, su ka koma cibiyoyin rajista ido-da-ido su ka yi kai-tsaye.

“Wasu 2,881,819 kuma sun kammala fara rajista a manhaja, amma ba su kai kan su cibiyoyin rajista ido-da-ido sun kammala ba.” Cewar Okoye.

Idan ba a manta ba, kwanan baya ne dai ƙungiyar SERAP ta jagoranci wakilcin mutum 24 waɗanda su ka shigar da INEC ƙara a Babbar Kotun Tarayya, Abuja, su na neman kotu ta tilasta wa INEC cewa ta ba su dama, su da sauran ‘yan Najeriya milyan 7 su kammala yin rajistar su da su ka fara.

A ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/1662/2022, sun shaida wa kotu cewa ba su samu damar kammala rajistar su ba har wa’adin da INEC ta gindiya za a rufe yin rajista ya cika.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shirin Tallafa Wa Manoma Mata ‘Yan Kasuwa Na GEEP Ya Kankama A Bauchi

Next Post

2023: Mace 1 Ce Ta Fito Takarar Shugaban Kasa Da Wasu 380 A Kujerun Majalisar Tarayya – INEC

Related

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

47 minutes ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

1 hour ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

3 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

4 hours ago
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

5 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

7 hours ago
Next Post
2023: Mace 1 Ce Ta Fito Takarar Shugaban Kasa Da Wasu 380 A Kujerun Majalisar Tarayya – INEC

2023: Mace 1 Ce Ta Fito Takarar Shugaban Kasa Da Wasu 380 A Kujerun Majalisar Tarayya - INEC

LABARAI MASU NASABA

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.