ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Tauye Wa Kowa Damar Mallakar Katin Zabe A Kasar Nan Ba – INEC

by Sulaiman
3 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta ƙaryata zargin ta hana mutum milyan 7 kammala rajistar mallakar katin zaɓe.

Sati ɗaya kafin jam’iyyun da su ka takarar zaɓen shugaban ƙasa su fara yaƙin nan zaɓen 2023, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce ba gaskiya ba ce zargin da ake yi ta tauye wa ‘yan Najeriya milyan 7 damar ƙasara rajistar da su ka fara ta manhajar INEC, domin mallakar katin rajistar zaɓe ba.

  • 2023: Mun Cire Sunayen Mutanen Da Suka Yi Rajistar Katin Zabe Sau Biyu —INEC

Cikin wata sanarwar da Kakakin Yaɗa Labaran INEC Festus Okoye ya fitar, ya bayyana cewa hukumar ta bayar da isasshen lokacin da duk wanda ya fara yin rajistar mallakar katin zaɓe a manhajar INEC, to ya je cibiyar yin rajista ido-da-ido ya kammala rajistar sa.

ADVERTISEMENT

Okoye ya ce duk waɗanda ba su kammala ba, ko dai sun fara ne su ka watsar, ko kuma sun fara, daga baya kuma ba su kammala ba, sai su ka koma a cibiyoyin rajista ido-da-ido domin su yi a can ɗungurugum.

“An jawo hankalin INEC dangane da wasu rahotannin da ake yaɗawa cewa ana zargin INEC da tauye wa mutum milyan bakwai damar kallama rajistar su ido-da-ido, wadda su ka fara a shafin manhajar INEC ta intanet.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

“To ya kamata a sani cewa a gaskiya INEC ba ta tauye wa kowa damar kammala rajistar mallakar katin zaɓe ba. Don haka rahotannin ba gaskiya ba ce, ƙarairayi ne kawai.

“Tun a ranar 24 ga Yuni, 2021 INEC ta ƙirƙiri tsarin fara yin rajistar mallakar katin zaɓe ta manhajar hukumar. Ta yi haka domin rage wa jama’a jeƙala-jeƙala da ɓata lokaci a wurin yin rajista ido-da-ido.

“A bisa wannan tsari, idan mutum ya fara rajista a manhaja, to daga baya zai samu lokaci ya je cibiyar yin rajista ido-da-ido, inda za a ɗauki hoton sa da tambarin yatsun hannun sa, domin kammala rajista, inda daga nan sai ya jira mallakar katin shaidar yin zaɓe (PVC).” Inji Okoye, wanda Kwamishina ne na Ƙasa, kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da kan Jama’a na INEC.

“Mutum 10,487,977 su ka shiga manhajar INEC domin fara yin rajista, amma a cikin su, yayin da 3,444,378 ne kaɗai su kammala yin rajistar a cibiyoyin rajista ido-da-ido.

“Daga cikin 7,043,594 waɗanda ba su kammala yin ta su rajistar a cibiyoyin rajista ido-da-ido ba, mutum 4,161,775 sun yi ƙoƙarin fara yin rajista ta cikin manhaja, amma sai su ka watsar, su ka koma cibiyoyin rajista ido-da-ido su ka yi kai-tsaye.

“Wasu 2,881,819 kuma sun kammala fara rajista a manhaja, amma ba su kai kan su cibiyoyin rajista ido-da-ido sun kammala ba.” Cewar Okoye.

Idan ba a manta ba, kwanan baya ne dai ƙungiyar SERAP ta jagoranci wakilcin mutum 24 waɗanda su ka shigar da INEC ƙara a Babbar Kotun Tarayya, Abuja, su na neman kotu ta tilasta wa INEC cewa ta ba su dama, su da sauran ‘yan Najeriya milyan 7 su kammala yin rajistar su da su ka fara.

A ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/1662/2022, sun shaida wa kotu cewa ba su samu damar kammala rajistar su ba har wa’adin da INEC ta gindiya za a rufe yin rajista ya cika.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Coas
Manyan Labarai

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Next Post
2023: Mace 1 Ce Ta Fito Takarar Shugaban Kasa Da Wasu 380 A Kujerun Majalisar Tarayya – INEC

2023: Mace 1 Ce Ta Fito Takarar Shugaban Kasa Da Wasu 380 A Kujerun Majalisar Tarayya - INEC

LABARAI MASU NASABA

Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.