• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Manta Da Irin Son Da Adam Zango Ya Nuna Min Ba – Tsohuwar Uwargidansa

by Rabilu Sanusi Bena
12 months ago
in Labarai
0
Ba Zan Manta Da Irin Son Da Adam Zango Ya Nuna Min Ba – Tsohuwar Uwargidansa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Na shiga wani hali sosai dan suma na rika yi, ‘yan gidanmu suna watsa mun ruwa ina farfadowa….” Kadan daga cikin kashi na biyu na tattaunawar da wakiliyarmu, RABI’AT SIDI BALA ta yi da tsohuwar matar Adam A. Zango kuma fitacciyar jarumar da ke taka rawa a yanzu cikin shiri mai dogon zango na Labarina a masana’antar Kannywood wato, AMINA UBA HASSAN, ke nan. Ga karashen tattaunawar kamar haka:

Mene ne ba za ki taba mantawa ba game da Adam A. Zango na dadi da na daci?

Eh! To, akwai abubuwa da yawa da ba zan manta da su ba, misali kamar; Irin son da ya nuna mun kafin ya aure ni har ya aure ni, da kuma kullen da ya nuna man ko bayan rabuwarmu, dan ina daya daga cikin matan Adamu da take kiran wayarsa kai tsaye, ko kuma idan yana wuri zan iya zuwa na same shi mu gaisa in ya ganni a guri zai tsaya mu gaisa za mu yi wasa da dariya to, abubuwa na dadi da ba zan manta da shi ba sunada yawa.

  • Kalau Nake Babu Abin Da Ke Damun Kwakwalwata – Adam Zango
  • Abin Da Ya Sa Nake Rungumar Ɗana Ina Wakar Soyayya – Tsohuwar Matar Adam Zango, Amina

Dan daya daga ciki ma zan iya cewa abubuwan girki ya koya mun wasu abubuwan a zaman aurenmu dan ya aure ni ina ‘yar karama na gama ‘Secondary School’, kuma a gida komai yi maka ake yi ba abin da ka ke yi, amma bayan ya aure ni ya koya mun wasu abubuwa dan shi ya iya girki, iya nawa shi ne; gyara gidana, ko ina tsaf-tsaf, na feffesa turare duk na iya wannan in yi wanka in yi kwalliya amma akwai abubuwa da yawa da ba za su kirgu ba na jin dadi da ba zan iya mantawa da Adamu a kan shi ba. Mara dadi kuma ‘I can’t see’ yanzu ba ma tare ba wani abu da zai iya yi mun ko na rashin dadi tunda ba wai muna tare bane.

Kin san an ce idan alkhairi ‘sometimes’ in mutum ya yi maka abu ka rika aunawa wanne ya fi yawa Alkhairin ko sharrin? To, alkhairin jin dadin ya fi rashin jin dadin yawa shi ya sa ban da wani abu na rashin dadi da zan fada gaskiya.

Labarai Masu Nasaba

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

Misali a ce yaronki yana son shiga harkar fim, shin za ki amince ya shiga ko kuwa ba ki da ra’ayin hakan a kan yaranki?

Idan dai har alkhairi ne ai sana’a ce ita ce mahaifinshi yake yi, ita ta mayar da shi abin da ya zama a yau, da kudin harkar fim aka auri uwarsa, da kudin harkar fim ake kula da shi tun yana karami har ya kai yanzu to, idan ya ce yana so iyaka a matsayina na mahaifiyarsa sai dai na bashi shawara na bi shi da addu’a, idan a san kaina ne ina son ya zama ‘Airpost officer’, ina so ya zama watarana, idan kuma fim yake ao yayi iya ka na bashi shawara na bishi da addu’a.

Idan mahaifinshi baya bukatar hakan a gare shi, shin za ki amince da maganar mahaifinshi, ko kuwa za ki goyi bayan danki?

Mahaifinshi ne, ai ba zai so yayi abin da zai bata rayuwarsa ba, abu ne na shawara, abu ne wanda ya zama dole ni da shi kuma daya shafi danmu mu tsaya mu yi shawara, dole zai ban dalilansa ni ma na ba shi dalilai na, idan na shi ya fi nawa falillahil hamd, idan kuma nawa ya fi nashi falillahil hamd, a karshe dai idan aka tsaya aka yi magana ta hankali dole dai zai zama an tsaya a matsaya guda.

Mu koma can baya, ya ki ka dauki fim a wajenki?

Na dauki fim sana’a, na biyu kuma ‘fashion’, saboda abu ne da nake yi nake kuma jin dadin yin sa.

Ko akwai wani kalubale da ki ka taba fuskanta bayan shigarki cikin masana’antar Kannywood?

Gaskiya babu wani kalubale dana taba fuskanta har zuwa yanzu, ban san dai gaba ba tunda ba a fata.

Wadznne irin Nasarori ki ka samu game da fim?

Nasarori gaskiya ba a iya kirga su, nasarori sosai fiye da tunani, na samu nasarori sosai ina ma kan samu, kuma ina fatan na ci gaba da samu in sha Allah.

Mene ne burinki na gaba game da harkar fim?

Burina nan gaba shi ne; Yau koda a ce nayi aure ya zama ina so na ga ina daraktin din fim ko da aure na. Wanda zan aure mutum ne wanda bai da matsala da koda nayi auren na ci gaba da fim dina, tunda sana’a ce, na dauke ita sana’a kuma zan rike mutuncin aure na to, amma ni dai ban fatan hakan, na fi so idan nayi auren nayi shi kenan.

Wane abu ne ya taba faruwa da ke na farin ciki ko akasin haka, wanda ba za ki taba iya mantawa da shi ba?

Ranar da dana ya sauke alkur’ani mai girma, yana daga cikin ranakun da ba zan taba mntawa ba, a ce yau yaron dana haifa a cikina na shayar ya sauke alkur’ani, ita ce ranar farin cikin da ba zan manta da shi ba. Na bakin ciki kuma shi ne ranar da ba zan taba mantawa da shi ba shi ne ranar da aka kwace Haider a hannuna na shiga wani hali sosai, dan suma na rika yi, ‘yan gidanmu suna watsa mun ruwa ina farfado wa, ina fita sai dai a dauko a dawo da ni cikin gida, na zama kamar wata mara hankali, saboda ba wai na san da za a karbe shi bane, kawai daga ya je yaho da babanshi ya dawo sai sakon babanshi na gani cewar ya rike Haider nayi hakuri.

Wannan ranar yana daya daga ranakun bakin cikin da na ji kamar na kashe kaina ma, sai kuma rasa iyayena guda biyu da nayi, na rasa mahaifiyata da farko ya zamana ba mu da wani gata daya wuce kakar mu, ita ta zama kamar Uwa ta zama Uba a gurinmu, ko babanmu yana nan ko baya nan ita ma ta zo ta rasu, sai daga baya Allah ya dauki ran mahaifina, ba zan taba mantawa da wannan ba a rayuwata.

Wace ce babbar kawarki cikin masana’antar kannywood?

Ba ni da babbar kawa a cikin masana’antar kannywood.

Bayan sana’ar fim kina wata sana’ar ne ko kuwa iya fim ki ka tsaya?

Kafin na fara fim inada shago ina shaloon, da turaruka da sauransu, kafin na fara fim ban saki shagon ba ina ‘planning’ wani abu akwai wani dan’uwana da yake ajjiya cikin shagon kowane shekara yana biya, akwai abin da nake.

Ya ki ke iya hada karatunki da kuma sana’ar fim, musamman yadda za ku bar gari domin daukar fim, shin hakan baya shafar karatunki ko ya abin ya ke?

Gaskiya yana shafa sosai duk da dai ni Alhamdulillah da akwai idon duniya in kana so ka ban tashin hankali ka ce mun karatu, bana shiri da karatu bana shiri da boko, kawai muna yinta ne saboda kwalin kawai muke bukata muna ganin gobe zai iya yi maka amfani ko ba ta gurin samun aiki ba zai iya yi maka amfani,

Me za ki ce ga masu kokarin shiga cikin masana’ar kannywood?

Kowa da sa’arsa yake zuwa, iya ka na ce su dauka sana’a suke yi kar su dauke shi kawai a ganni a TB, su yi shi da soyayya, su dauke shi sana’a sosai. Idan suka dauke shi sana’a to, shi ma zai dauke su ‘actors’.

Wane sako ki ke da shi ga masu kallo da kuma masoyanki?

Ni masoyana ba abin da zan iya fada musu na nuna musu ‘how appreciate like’ dadin yadda nake jin dadin kaunar da suke nuna mun, ba abin da zan ce musu sai dai kawai na ce Allah ya saka musu da alkhairi kuma su ci gaba dan yanzu aka fara, ina so na gode musu dan godiya ‘to me isn’t enough’ kamar yayi kadan saboda irin son da suke nuna mun, sai dai na ce na gode Allah ya saka musu da alkhairi.

Misali wani cikin masana’antar kannywood ya nuna yana sonki kuma zai aure ki, shin za ki amince da hakan ko kuwa ba ki da ra’ayin hakan?

Gaskiya ba zai ma iya faruwa ba, ba ni da ra’ayin haka, auren wani dan kannywood ban ma sa shi ma cikin ‘calculation’ din rayuwata ba, wancan dai Allah ya yi za a yi kuma an yi, amma ba za a kara ba, ban da wannan ra’ayin, ban ma taba tunaninshi ba, dan ba abu ne da zai yu ba.

Me za ki ce da masu karanta wannan hirar taki?

Muna godiya da karanta hirarmu da suke yi ‘because’ wani lokacin ta nan ne wasu suke sanin wane ne jarumin da suke so ko ba sa so.

Ko kina da waɗanda za ki gaisar?

Wanda zan gaisar ba za su wuce masoyana ba, masu nuna mun soyayya wasu ma da ban san su ba, ba su taba ganina ba, wasu ba su sanni ba, ba su san ya nake a zahiri ba, amma duk da haka suke so na, su kadai zan gaisar in ce musu duk ina gaishe su kuma ina godiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abdullahi AdamuHausa FimKannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sallah Babba: Gwamnatin Uba Sani Ta Kula Da Almajirai A Jihar Kaduna

Next Post

Kitson Sallah

Related

DSS
Labarai

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

2 hours ago
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

3 hours ago
katsina
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

4 hours ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

6 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

17 hours ago
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

20 hours ago
Next Post
Kitson Sallah

Kitson Sallah

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.