• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kasuwar Sin Na Ci Gaba Da Jan Hankalin ‘Yan Kasuwar Kasa Da Kasa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasuwar sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne, aka fitar da alkaluman kididdigar tattalin arzikin kasar Sin, wanda ke nuna karuwar yawan hajoji da kayayyakin masarufi da Sin ta sayar, zuwa kashi 4.6 cikin 100 kan na shekarar bara, wanda ya karu da kaso 2.1 cikin 100, fiye da na watan da ya gabata. Wannan na kara tabbatar da cewa, alkaluman tattalin arzikin kasar Sin sun inganta, kuma cinikayyar hajojin kasar ta zarce yadda ake zato. 

Sanin kowa ne cewa, baya ga wadannan alkaluma, akwai kuma damarmaki na yin kasuwanci da baki daga waje ke sha’awa matuka. Tun daga farkon wannan shekara, farfadowar tattalin arzikin duniya yake fuskantar tafiyar hawainiya, kuma sakamakon durkushewar manufofi a manyan kasashe masu karfin tattalin arziki ya fito fili.

  • Sin Da Zambia Na Samun Ci Gaba A Fannin Bunkasa Yankin Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki

Amma abin farin ciki shi ne, tattalin arzikin kasar Sin ya jure matsin lamba, ya kuma ci gaba da farfadowa, kuma yana ci gaba da zama muhimmin injin na ci gaban tattalin arzikin duniya. Lamarin dake kara baiwa ’yan kasuwa daga sassan duniya karfin gwiwa da sha’awar kara shiga babbar kasuwar kasar don gudanar da kasuwanci da samun babbar riba.

A bangaren masana’antun kasa da kasa kuwa, wani abu mai muhimmancin gaske shi ne kyakkyawan fata a lokacin da kasuwar duniya ke fama da rashin tabbas. Yayin da wasu makiya ke yada bayanai marasa tushe game da tattalin arzikin kasar Sin, bankin duniya ya yi hasashen cewa, a bana tattalin arzikin Sin zai bunkasa da kaso 5.6%, yayin da OECD kuma ya yi hasashen bunkasar za ta kai kaso 5.4%, kana Asusun ba da lamuni na duniya IMF, ya yi hasashen bunkasar zuwa kaso 5.2%.

Masu fashin baki na cewa, kwanciyar hankali da dorewar manufofin tattalin arzikin kasar Sin, sun karfafa gwiwar kamfanonin kasa da kasa wajen kara neman shiga babbar kasuwar kasar. Sun kuma yi imanin cewa, kasar Sin na daya daga cikin manyan kasashe a duniya da ke samar da damammakin ci gaba ga kamfanonin kasa da kasa. (Ibrahim Yaya)

Labarai Masu Nasaba

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Jami’in CPC: Sin Da Cuba Za Su Goyi Bayan Juna Kan Batutuwan Da Suka Shafi Muhimman Muradu

Next Post

Sin Ta Zarce Amurka A Yawan Takardun Bincike Masu Kima

Related

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro
Daga Birnin Sin

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

5 minutes ago
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

20 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

21 hours ago
Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu
Daga Birnin Sin

Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

22 hours ago
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

2 days ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

2 days ago
Next Post
Sin

Sin Ta Zarce Amurka A Yawan Takardun Bincike Masu Kima

LABARAI MASU NASABA

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

August 11, 2025
Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

August 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

August 11, 2025
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.