• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Dalilin Fargaba Ko Tsoro Don Sanya Wa Mara Lafiya Robar Hanci

by Sani Anwar
4 months ago
in Kiwon Lafiya
0
Babu Dalilin Fargaba Ko Tsoro Don Sanya Wa Mara Lafiya Robar Hanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna

Robar hanci (Nasogastric tube), wani siririn tiyo ne na roba; wanda ake zira shi ta kofar hanci har zuwa cikin tunbi. Manufar ita ce, don a samu kai wa ga cikin tunbi.

Sanya robar hanci, na iya zama cikin muhimman ayyukan taimakon gaggawa; yayin da aka garzaya da mara lafiya zuwa asibiti.

  • Kauyuka Suna Kokarin Neman Cimma Burin Samun Wadata Tare A Kasar Sin
  • Bukatar Sanin Hakikanin Halin Da Tattalin Arzikin Nijeriya Ke Ciki

Haka nan, sanya robar hanci na da muhimmancin gaske ga mara lafiya kamar haka:

1- Ana amfani da robar hanci, domin ciyar da abinci ko shayar da abin sha ga mara lafiya, musamman a halin da mara lafiya ya tsinci kansa na rashin iya cin abinci ta bakinsa; ko dai saboda mara lafiyar ya ki ci ko ya ki sha ko saboda miki ko rauni a bakinsa ko kuma bayan tiyata a baki ko kuma a makogwaro.

2- Ana amfani da robar hanci, domin bai wa mara lafiya magunguna kai tsaye zuwa cikin tunbinsa, musamman ga mara lafiyar da ke fuskantar wahalar hadiya ko kuma ba zai iya karbar magani ta baki ba.

3- Ana amfani da robar hanci ga mara lafiyan da ya fita daga hayyacinsa, ko dai saboda wata larura ko kuma allurar kashe-ciwo da ake yi kafin tiyata.

4- Haka nan, ana amfani da robar hanci domin kiyaye wa mara lafiya shakar abinci, abin sha, majina ko kuma yawu zuwa cikin huhunsa, musamman ga mara lafiyan da ya gaza hadiyar abin ci ko sha yadda ya kamata; kamar masu shanyewar barin jiki, buguwar kai da sauran makamantansu.

Domin shakar abinci ko abin sha, majina ko yawu zuwa cikin huhu; na da hadarin gaske. Sau da yawa, ba larurar da ta kwantar da mara lafiya ce ke sababin mutuwarsa ba; face illolin shakar wadannan abubuwa zuwa cikin huhu. Hakan na nufin wahalar shakar oksijin.

5- Har wa yau, ana amfani da robar hanci wajen zuke gurbataccen abinci ko abin sha, iska, diwa ko jini daga cikin tunbi.

6- Bugu da kari, robar hanci na amfani wajen bude hanya; bayan toshewar hanyar makoshi daga baki zuwa cikin tunbi.

7- Bayan nan, ana amfani da robar hanci kafin ko bayan tiyata a ciki da dai sauran wasu dalilai daban-daban.

Sai dai, sanya robar hanci ga mara lafiya na daga cikin abubuwan da ke sanya tsoro da fargaba a zukatan ‘yan’uwa da abokan marasa lafiya, saboda yadda ake zaton cewa; ba a sanya robar hanci ga mara lafiya, har sai ya kai gargara.

Sau da dama ma, wasu na canfa cewa; matukar aka sanya wa mara lafiya robar hanci, to fa ba zai dawowa gida ba; ma’ana mutuwa zai yi.

Amma kwata-kwata, abin ba haka yake ba. Domin kuwa, ana sanya wa marasa lafiya robar hancin ne kadai; idan bukatar hakan ta zama dole, sannan kuma sanya ta ga mara lafiyar wani gagarumin taimako ne domin ceto ransa.

Har ila yau, ana sanya robar ne na dan wani lokaci gwargwadon bukata, sannan a cire bayan bukatar ta gushe.

Bugu da kari, babu wani dalilin tsoro ko fargaba; idan aka sanya wa mara lafiya robar hanci, domin yin hakan shi ne abin da zai fi amfanar da lafiyarsa a daidai wannan lokaci.

Allah ya ba mu lafiya da zaman lafiya, marasa lafiyar kuma na gida da na asibiti, Allah ya ba su lafiya; ya kuma tashi kafadunsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AsibitiHanciRashin LafiyaRobar
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (3)

Next Post

Ƴansanda A Gombe Sun Yi Holar Masu Laifuka

Related

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

3 days ago
Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna
Kiwon Lafiya

Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna

2 weeks ago
Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta
Kiwon Lafiya

Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta

1 month ago
Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam
Kiwon Lafiya

Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam

2 months ago
Shawarwari Kan Kayyade Amfani Da Siga
Kiwon Lafiya

Shawarwari Kan Kayyade Amfani Da Siga

2 months ago
Amfanin Aduwa Ga Lafiyar Ɗan Adam
Kiwon Lafiya

Amfanin Aduwa Ga Lafiyar Ɗan Adam

3 months ago
Next Post
Ƴansanda A Gombe Sun Yi Holar Masu Laifuka

Ƴansanda A Gombe Sun Yi Holar Masu Laifuka

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.